Rumbun Qaya page 75

 

Rumbun Qaya page 75

***RQ***


Hafsat Rano


    page 75


         Last Page😭



***Direct asibitin suka wuce, suna zuwa ana fito da Babyn. Raihana ce a gaba wajen riga karbar ta daga hannun gwaggon Khadijan, a rayuwar ta tana balain son yara musamman tunda ta taso Itace karama babu wani yaro da take gani ko ta dauka. Kwakume yar tayi a jikinta wadda tayi mata kama da Aryan dinta sosai zaka rantse da Allah shine ya Haiti babyn. 


“Raihana bawa kowa ya dau babyn mana.”


Ammy tace gani ta rike ta hana kowa, bata ma Ankara ashe rike bbyn tayi ba sai da ammyn tayi magana, a kunyace ta mika ma su Ya nabeela ita, ita kuma ta mikawa ammyn suka daddauka suna mata addua.

   Aryan yana tare da Kamal dan tun a gate din Asibitin suka hadu ya dawo daga siyo wata allurar (RhoGham) a waje da ake ma duk masu negative Rhesus (Rh negative )na jini wadda aka son ayi ta around 26-28weeks of pregnancy sannan a sake yi within 72hours idan mace ta haihu idan aka tabbatar da babyn Rh positive ne. Da farko asibitin sun zata suna da ita sai da suka duba suka ga basu da ita sannan suka ce yaje ya siyo ta shine abinda ya fitar dashi din har akayi haihuwar baya wajen. Rike da hannun juna suna magana suka karasa ciki, suka wuce wajen nurses din suka basu sannan suka dawo wajen da su Ya nabeelan suke.

   Ya nabeela ce ta fara hango su, tayi saurin karasawa ta rungume Aryan din, wanda yake ta faman murmushin jin dadin ganin ta


“Maman Aryan ni fa?” Kamal yace yana dariya


“Matsa nan wa yake ta kai naga boy dina.”


“Boy? Wannan sangamemen magidancin katon ne boy?”


“Ko shekara nawa Aryan zai a wajena boy ne.”


“Hum hmm, lallai zaa sha kunya kuwa kwanan nan, dan nasan kin kusa jin kukan babies.”


Yace yana dariya sosai. Shi dai Aryan be ce komai ba, sai hararar Kamal din kawai yake suka karasa wajen da sauran suke ya russuna har kasa ya gaida gwaggon khadija Sannan ya sake gaida su Ammy a karo na biyu. Bbyn aka mika musu yayi saurin karbeta ya riga Kamal din yana kallon kyakkyawar fuskar ta. Lekowa Kamal yayi sai ya rike baki


“Kaga kama ko?” Ya nabeela tace


“Exactly fa.”


“Jini malam.” Yace yana murmushi. 


“Wannan mommy na ce, ni zan mata huduba.”


“Kaine ma babanta ai.” Kamal yace yana dariya


Waje aryan din ya samu yayi mata huduba nan take da sunan Nana Khadija, ta zama yar khadija jikar khadija kuma khadija. Sai a sannan ya mikawa Kamal din ita yana cewa


“Ba dan halin ka ba.”


“Nagode.” Ya karbeta yana kallon fuskar ta. Waigawa Aryan yayi yana neman in da raihana ta shige, bata wajen tunda suka karaso.


“Tana ciki wajen mejego.”


Sosa keyar sa yayi a kunyace ya bar wajen ya matsa wajen kamal da yake ta kallon babyn. Sai Ya tuna misscarrige din da khadijan tayi a wanchan lokacin, suka shiga yanayi saboda yadda suka kwallafa rai akan babyn, sai gashi Allah ya sake basu.

  Ya nabeela ya bawa bbyn tace su shiga da ita ciki khadijan ta ganta itama dan bata ganta ba. Cikin dakin suka shiga tare da Aryan, raihana na zaune a gabanta suna magana ita kuma tana kwance ta dan sha wahala sosai ta zubar da jini shiyasa suka dan riketa a cikin ma. Tashi raihana tayi da sauri da suka shigo ta dan buge da kujerar da take kai, da sauri Aryan ya riko ta ganin kamar zata fadi.


“Wow… haka kake dama?” Kamal yace yana zama a kujerar da raihanan ta tashi.


“Faduwa fa ta kusa yi, Allah Ya Rufa asiri idan ta fadi za’a iya samun matsala.”


“Ko? Haka ne kuma gaskia, sannu kanwata ki dinga kula kinji?”


“In sha Allahu, ina wuni?”


“Lafiya lou, an dawo lafiya?”


“Alhamdulillah, an samu karuwa, Allah Ya raya.”


“Amin kunyi ‘ya, gata nan dan wayo sai ta kwaso mijinki.”


“Ta kyauta ai.”


“Ai shikenan.”


“Sannu.” Yace ma khadijan yana rike da hannun raihanan, suka gaisa sannan suka juya suka fito suka bar musu dakin dan suna da bukatar kebewa. Suna fitowa ya tsare ta kofar


“Let’s go home please.”


“Ba’a sallame su ba fa, mu dan jira.”


Tace tana satar kallon bangaren da su Ammy suke amma duk basa kallon su wani wajen daban suke kallo


“No tafiya zamuyi, kin gaji kina bukatar hutawa.”


“I can manage Allah, please mu jira a sallame su.”


“A ah, muyi gaba zasu taho daga baya, after wannan long journey din Kina bukatar ki huta sosai, ba ki kara wata gajiyar ba.”


“Kai fa? Baka kaji ba?@


“Ni I’m a man.”


“Please.”


“Noo. Muje kiyi musu sallama.”


Marairace fuska tayi, yaki kallon ta yayi gaba, bin sa tayi kamar zata fashe da kuka, bata so ta tafi har ga Allah, wajen su ammyn ya isa yayi musu sallama sannan suka yi gaba shi da Ya nabeela suna magana. Tana karasowa Ammy tace


“Ai gwara kuje ku huta, wannan uwar tafiyar haka.”


“Ni nafi so mu tafi daku, na dade fa bana nan.”


“Kaji min yarinya, kin tashi kin bi mijinki ko sai na buge ki?”


“Dadah! Nice fa? Raihanan ki.”


“Idan ba zaki bi umarnin mijinki ba, tsaf zan ajiye komai na dumama miki jikinki ehe.”


“Kowa baya so na.” Tace wani kuka na taso mata, haka kawai taji kukan kuma ba gaira ba dalili. Basu goya mata baya ba, haka ta tashi suka bita da kallo tana matse kwalla saboda takaici.

  A jikin mota ta tarar dasu shi da Ya nabeela suna magana, kin kallon ta yayi data karaso dan tunda ta nufo su ya lura kuka tayi.


“Sai mun shigo gidan kanwata.” Ya nabeela tace tana matsawa daga jikin motar, shine ya bude mata da kansa ta shiga gaban motar sannan ya zagaya ya bude wajen driver ya shiga ya zauna


“Naga kamar an chanja motar nan.”


“Itace dai, gyra tasha kasan ni da ita akwai amana.”


“Ah gaskia ne. Tayi kyau kuma sosai.”


“Nagode, sai mun shigo.”


“Ok.” Ya yi ma motar key suka fita daga asibitin. 


  Tunda suka dauki hanyar gidan babu me magana a cikin su, kowa yayi dip shi rigimar tace baya so gashi yana driving baya son raba hankalin sa, ita kuma haushin ta yaki kulata bare tayi masa darun nata. Cika tayi fam ta hau kamar flour wa, ga wani irin rauni da zuciyar ta tayi kamar ta zauna tayi ta zunduma ihu, ta zama so emotional kwanakin nan abu be kai ya kawo ba sai tayi masa kuka, ga saurin fushi wanda da ba haka take ba. 

   

“Me zaki ci?” Ya tambaye ta hankalin sa na bisa titi be kallo side din ta ba


“Babu komai.” Tace a gajarce. Be sakè magana ba, ya dauki hanyar gidan su kai tsaye, wanda yake so yaga irin gyaran da akayi masa da Ya nabeela tace masa maganar. 

   Tun daga kan layin ya tabbatar da an gyara gidan dan har fenti akayi masa me kyau da tsada. Ita raihana ma bata gane gidan ba sai data ga yayi horn a gate din gidan sannan ta gano. Da sauri Baba maigadi yazo ya bude yana ganin aryan din ya cika da murna da farin ciki, yayi saurin wangale gate din suka shiga harabar gidan da aka kusan sauya mata fasali aka kawata ta da wasu manyan flowers masu girma da kyau.


“Sannu da zuwa ranka ya dade.” Baba me gadi da ya karaso yace yana dan dukawa


“Baba, barka da gida.” Ya kashe motar ya fito sannan ya mika masa hannu suka yi musabiha, sannan suka sakè gaisawa. Suna gaisawar raihana ta wuce su zuwa ciki bayan tace masa ina wuni a gajarce. Tana shiga ta cire veil din sannan ta zare rigar jikinta ta watsar dukka a falon saman kujera ta wuce ciki da sauri ta shiga toilet ta kunna ma kanta shower, ta saka kuka.

   A falon ya zauna ya mike kafarsa da tayi masa wani irin nauyi, gajiyar da yake ciki ya duba ya auna da tata yasan definitely ta fishi gajiya gashi baya son wani abu ya faru da ita shiyasa yake kaf kaf da ita har zuwa sanda abinda yake zargin zai tabbata, ya lura sarai da yadda hanata zaman ya bata mata rai ya kuma yi mata uzuri dan ba halin ta bane ba, duk cikin signs din ne dan haka zai lallaba ta a hakan har Allah ya kawo karshen. Jin shiru shiru bata fito ba yasa shi mikewa yabi bayan ta zuwa saman ya hau yana kiran sunan ta, shiru babu alamun tana saman sai ya sauko zuwa bedroom din kasa ya tura kofar ya shiga. A chan saman gadon ya hange ta, tayi dai-dai a saman gadon ta kure ac dakin tana baccin ta hankali kwance. Towel ne kawai a jikinta wanda ya bayyana ilahirin cinyoyinta farare tas. Girgiza kai yayi ya karasa ya gyara mata towel din, sannan ya ja mata kofar ya fita zuwa sama, bayan ya dan lalleka yaga gyaran da akayi ma gidan wanda bashi da maraba da sabo, hatta furnitures da komai an zuba, kayan kitchen da kayan abinci dankare a store. Yana shiga dakin su na saman ya tarar da akwatunan raihanan dozen cif, guda shida golden sai shidan kuma Blue black. Wuce su yayi ya watsa ruwan shima sannan ya zauna ya dauki wayar sa yayi musu Order abinci daga Albaik Restaurant, ya zura slippers ya fita ya samu Baba megadi ya fada masa zaa yi musu delivery ya karba sai ya ajiye ta kofar baya na kitchen din. Ciki ya koma zuwa dakin da take, ya rufe kofar ya saki curtains din ya haye gadon gami da jawo ta jikinsa ya rungume ta, dan shima baccin zai dan yi ko babu yawa.

   

***Ita ta fara tashi ta zare jikinta wajen laasar, tana mikewa ya farka sai ta kauda kanta da sauri ita a lallai fushi take dashi, dariya ta bashi ya murmushi kawai yana dan kulle idonsa bacci ya sake shi sosai. Fitar ta yasa shi bude idon yabi kofar da kallo, sai ya mike ya shiga toilet din yayo alwala yazo yayi sallah a dakin dan an idar a masallaci, sannan ya fito falon ya tarar da ita, ta saka doguwar riga tana cin abinci, gefen ta ya zauna ta dan matsa ya sake matsowa ta sake matsawa sai ya karbe abincin ya ajiye ya jawota jikinsa. Shar shar shar sai hawaye, 


“Na banu.” Yace kasa-kasa 


“Fushi kike dani?”


Daga masa kai tayi, ya sa hannun sa ya share mata hawayen fuskar


“Ya isa toh, ba zan sake ba. So nake ki huta sosai. Kinga har baccin ki, kika samu kikayi.”


“Ni nafi son wajen su Ammy, na dade fa ban gansu ba.”


“Ai zaki je, tunda mun dawo sai kin gaji da zuwa ma.”


“Ni yau nake so.”


“Toh shikenan, anjima da daddare sai muje ko?”


“Eh.” Ta gida masa kai


“Good girl.”


“Bani abincin toh.”


“Glut…” da sauri ta kalle shi, sai ya rufe bakin sa ya girgiza kai


“Wasa nake ba ke ba, bari na baki a baki Hajiya ta.”


Dauko plate din yayi, ya shiga bata a baki tana ci a hankali, ta gama ya bata juice me dan sanyi tasha da ruwa sannan ya zuba nasa shima yaci.



***Da wayo da wayo suka fasa zuwa gidan yau kamar yadda yayi mata alkawari, daddy da Abby ma sai waya sukayi musu suka gaishe su kafin su shigo gobe. Basu san abinda ake shirya musu a gidan ba, basu kuma san yadda komai ya kusan dawo daida ba duk da har yanzu Daddy na ta faman bin Abby akan ya dawo company su cigaba da harkar su tare Amma sam yaki, shi kuma yaki hakura sai mutane yake tura masa amma fafur yaki. Dawowar su Aryan din nan yasa Daddyn yanke shawarar tura ma Abbyn su, su rokar masa shi wala Allah idan su ne ya amince. Apart from wannan komai tare sukeyi ko yaushe kuma suna tare a gida ko a SABUWAR majlisar su da suke zama a kofar gidan Abbyn da daddare suci abinci suyi hira. 

   Yau rana ce ta musamman ga ahalin biyu, ga haihuwar matar kamal ga dan kwarya kwaryan bikin da Daddyn ya shirya ma su raihanan a matsayin murnar auren su da ba’a samu anyi ba, sannan da dawowar familyn nasu waje daya.


Casual dress dinsu suka saka shi riga shirt da wando sai pcap da ya dora saboda ranar da ake kwallawa, ita kuma tasa normal doguwar rigar atamfa ta yafa medium veil sai shoe and bag. Da gidan su Aryan din suka fara daga nan sai su wuce gidan ammyn in da zai barta a chan har dare sannan yazo su tafi gidan Kamal su sakè ganin babyn, da shirin kwanan ta a gidan su ta taho ba tare da ya sani ba shi sam, suna zuwa gidan su sai suka tarar da Ammy, Daddy, Abby, Dadah, Kamal, Lamido, Sadeeq, hydar, Ya Nabeela a gidan suna jiran isowar su.

  Dadi kamar zai kashe raihana, ta rasa in da zata saka kanta saboda farin ciki, a babban falon suka taru dukkanin su, akayi ma Mommy addua sannan Abby ya fara magana akan hadin kansu da yarda da juna, ya gama Daddy ma yayi nasa ammy dai tace ba sai tace komai ba, daga nan ne kuma su matan suka shiga ciki suka bar mazan a falo in da suka zauna zaman cin abinci masu rai da lafiya, ana ci ana hira tsakanin iayyen biyu sai suma mazan suna nasu daga gefe, maganar auren Hydar da Lamido suke tattaunawa wanda har an saka date shi sadeeq tasa bata kasar tana Jordan tana karatu amma ta kusa kammalawa shisa aka daga nasa zuwa sanda zata dawo. Dama shi ba gwanin magana bane sosai he’s cool bashi da hayaniya ko kadan. Hydar ne dama me magana ma a cikin su dan Lamido ma kusan hakan yake, sai ya zama kamal da hydar ne kawai ke rike da wajen su sauran sai eh da a ah sai yar magana wadda bata cika wani tsawo ba. 

  Har dare dukkanin su suna tare, hakan ya kara shakuwa sosai tsakanin su, wanda suka yanke zaa dinga irin zaman haka duk karshen wata aji uzurin juna da damuwar juna. Da aka zo zaa watse daddy yace yana da magana, anan ya sake bijirowa da Abby da hydar tayin dawowa su cigaba da Aiki tare, tunda shi Lamido aikin sa babba ne haka ma babbo sadeeq likita ne a babban asibiti sai dai idan yana da bukatar transfer wanda bashi da ma raayi chan ya saba chan zai zauna dama kuma Dadah ta kusa tattarawa ta koma gida shikenan bashi da matsala tunda akwai Dadan su. 

   Idanun yaran ya hana Abby sakè rejecting offer din Daddyn amma har ga Allah be so ba, yaso ace ya barshi kawai hakan ma ya ishe shi, amma idan yaki sai yaran su ga kamar be yafe abinda ya faru bane ba.


“Shikenan Allah ya kauda fitina a tsakani.”


“Alhamdulillah, naji dadi sosai aminina. Nagode sosai.”


“Hydar fa?”


“Eh toh, gashi nan a zaune, dama shi Yarinyar da zai aura yar kanwar ammyn su ce, amina. Idan yaga zai tattaro ya dawo nan din gaba daya saboda karatunta ma toh, idan kuma ya zabi chan ba zamuyi masa dole ba.”


“Zai dawo ma.” Aryan yace kai tsaye kamar shi aka tambaya


“Waye Ya amsa ne wai?” Daddy yace yana kallon su


“Aryan ne.”


“Barshi daddy, ya ari baki na ya ci min albasa,Allah ya tabbatar mana da allhairi.”


“Toh Amin Amin.”


Su Abby ne suka fara tafiya tare da  Hydar da Babbo Sadeeq , Lamido kuma ya dauki ammy da dadah. Raihana kamar tace zata bisu amma sai ta daure, ta buya ta share kwallarta. A Yanzu ne yake da bukatar zama tare da yan uwanta da iyayenta. A tare irin zaman da suka rasa a baya, amma bata so ta nuna damuwar ta a fili ga Daddy ga Ya nabeela. Dole ta shanye suka yi musu sallama suka tafi. Duk da dare ya fara yi sai da suka je gidan Kamal din, suka ajiye shi sannan suka sakè ganin baby sannan suka tafi.

   Dakin da akwatunan suke ya jata, kadan ya rage ta sangame saboda tsabar mamaki, zaunar da ita yayi ya shiga bude mata su daya bayan daya tana kalla, tun tana zaune har ta mike ta sake zaunawa ta rasa ina zata saka kanta saboda tsabar farin ciki


Kwana hudu da fara azumi ta soma laulayi na sosai, wanda har sai da ta kwanta a asibiti aka sa mata drip saboda galabaitar da take yi wajen amai.


*****Bayan Wani Lokaci🤪


Rayuwa ta cigaba da garawa cikin hukuncin Allah, komai yayi farko dama zai yi karshe, sannan duk nisan jifa kasa zai fado. Rayuwa ta sauya sosai a familyn Nasir Matawalle da amini shakikin sa IBRAHIM Mukaddas, kamar yadda suke a shekarun baya hakan ma yanzu suke , sun sake dinkewa koman su tare su ke yi, sannan yaran su sun zama yan uwan juna tamkar yadda suke a dah, kowa Ya dauki uzurin kowa ya dora a bisa kansa, duk abinda ya shafi daya ya shafi dukkansu. Suna matukar girmama juna da kaunar junan su. Hydar, Lamido da sadeeq duk sun yi auren su, suna zaune lafiya da matayansu gwanin shaawa basu wata Matsala haka kamal da matar shi. Haka uwar gayya Ya nabeela da nata familyn itama. Abby da ammyn sun dawo kusa da Daddy ga gida ga gida kamar yadda suke a da, tsohon gidan su raihanan kuma wanda yake jikin gidan su na yanzu Kamal ne da Hydar aka gyara musu shi aka fitar ma kowa da part dinsa daban da gate dinsa suke zaune, hakan ya kara shakuwar su ya kuma dawo da tsohuwar abota tsakanin hydar da Aryan dan kullum suna tare a gida ko a Office.


   A bangaren Adam, ya fito bayan daddy ya yi magana da Lamido akan akan case din an kuma duba laifin nasa an hukuntashi daidai da laifin sa sannan ya biya tara wadda Daddyn ne ya biya. Haka shima Muhammad akayi da Zainab aka kaisu court aka yanke musu hukuncin su daidai da laifin da suka aikata. 


Ita kuwa me gayya me aiki, uwar mugaye da tsinannu duniya ta gamu da daidai da abinda ta aikata domin sai da aka sake mata aikin kafar aka sakè yanke ta har zuwa cinya Ya zama baki daya bata da kafa kwata kwata, ga haukan da ya sake mata karfi sosai daga Akth din dawanau aka wuce da ita aka bata daki ita kadai saboda yadda take fizgar gashin kanta da yadda take yaga kayan da duk aka saka mata tana surutai tana tonawa kanta asiirin abinta ta aikata a baya, sau daya Aryan suka je da raihana suka ganta Raihana sai da tayi kuka shi kuwa Aryan ko gezau zuciyar shi ta riga ta bushe. Shi dai tunda burin sa ya cika dan hatta barrister din nan da sukayi aiki tare da Hajiya zeenat din sai da aka kamo shi aka yanke masa hukunci daidai dashi. Zuwan Aryan ya sake rikitata, ta dinga kiran sunan sa tana cizgar gashin kanta, daga ranar aka hana kowa ma zuwa ganin ta.


******Tana tsaye a jikin sink din kitchen tana wanke bowl din cereal din Hanan, suka shigo ya doro ta a saman kafadar sa tana ta yi masa gwaranci. Dogon wando cotton ne a jikin sa babu ko riga suka shigo kitchen din ya dora Hanan a saman cabinet din kitchen din ya riko kugun raihanan ya juyo da ita suka saka dariya a tare


“Kai da yarinyar ka kun fiye rigima wallahi, ina zaman zama na kun sani Aiki.”


“Ya zaki damu? Umm?”


“Bada sadakar ku zanyi na huta kawai.”


“Ke Babyna, Yanzu zaki iya bada mu sadaka? Kalle mu fa, innocent babies dinki.” 


“Ga shi nan ai, face dinka ne da ita.  Ku narke ma mutum ido ko be niyyar abu ba yayi muku.”


“Eh Munji, Yanzu dai a bamu abincin mu, idan kuma muka ga dama muce a mana wani daban.”


“Allah ya baku hakuri, tasha friso din yanzu dai.”


“Nifa me zaki bani?”


“Ko zaka sha oat?”


“Um um, ni sai dai ki bani wannan.”

 

Ya nuna kirjin ta, 


“Kana da matsala.” Tayi saurin daukar gwangwanin friso din da bowl din ta zame ta barshi a tsaye yana mata dariya. Daukar yar su yayi suka koma falo still yana dariya a hankali. Ta fito ta ajiye masa bowl din a gabansa tasa spoon tace


“Gashi nan.”


“Mun gode Mamin mu.”


Ya kwaikwayi karamar murya ya fada, murmushi tayi ya mayar mata, tayi hanyar bedroom dinsu tana cigaba da murmushin 








Alhamdulillah!!! Dukkan godiya ta tabbata da Allah ubangiji, da ya bani ikon kammala wannan littafin wanda ya ja ni har zuwa in da ban yi zato ko tsammani ba, ina rokon dukkannin wanda na batawa da ya yafe min, ina kuma fatan kun amfana da wani Darasi a ciki komai kankantar sa


Duk abinda kuka gani na kuskure ku dauke shi a matsayin ajizanci na dan Adam. Allah ya shirya mana zuri’ah ya raba mu da sharrin masu sharri, ya hada mu da masu son mu na gaskiya ya yafe mana zunuban mu. Sai watarana idan allah ya Kaddara saduwar mu. Nagode Nagode Nagode. Zafafa biyar na matukar godiya. Na yafe ma duk wanda Ya bata min.


Ma’assalam. Rano😍

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post