Yanzu-yanzu: Osinbajo ya gana da shugaban APC, da gwamnonin Jam'iytar

 Mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo, na ganawa da shugaban jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Adamu da gwamnoni biyar na jam’iyyar a daren ranar Alhamis.


Taron dai yana gudana ne a fadar shugaban kasa dake Abuja.

A bayanan da Jaridar LEADERSHIP  ta hada yana cewa taron ba zai rasa nasaba da zaben fidda gwani na shugaban kasa na jam’iyyar da za a yi ranar Litinin mai zuwa ba.

Ku tuna cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da gwamnonin a ranar Talata kafin ya tafi kasar Spain domin ziyarar aiki.

Ana kuma sa ran shugaban kasar zai gana da gwamnonin jam’iyyar APC da suka dawo daga tafiyar a ranar Juma’a domin cimma matsaya daya gabanin babban taron jam’iyyar na kasa na musamman.

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post