Yan bindiga sunyi garkuwa da Shugaban Kwalejin Kididdiga dake Manchok, Kaduna.

 

Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kai hari makarantar kididdiga ta tarayya da ke Manchok, karamar hukumar Kaura a Kaduna a daren Talata 2 ga watan Agusta da misalin karfe 9:00 na dare.

‘Yan bindigar sun kashe mutum daya tare da yin garkuwa da mutane biyu; ciki har da shugaban makarantar.

Harin dai ya zo ne makonni uku kacal bayan an kashe wasu ma’aikatan wucin gadi biyu da ke kula da raba gidajen sauro a hanyar Zangang zuwa Zankan a karamar hukumar.

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post