Shugaban Kasa Buhari ya rantsar da sabbin Ministoci

 Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari ya rantsar da sabbin ministoci bakwai da Majalisar Dokokin ƙasar ta tatance.

Ya rantsar da su ne gabanin taron Majalisar Zartarwar ƙasar na mako-mako Larabar nan.

Ministocin ta aka rantsar sun hada da Umana Okon Umana daga jihar Akwa-Ibom a matsayin ministan Naija Delta, da Ikoh Henry Ikechukwu daga jihar Abia a matsayin ƙaramin ministan kimiyya da fasaha, da Umar Ibrahim El-Yakubu daga Kano a matsayin ƙaramin ministan ayyuka da gidaje.

Sauran kuma su ne Goodluck Nanah Opiah daga jihar Imo, wanda ya rabauta da kujerar ƙaramin ministan ilimi, da Ekumankama Joseph Nkamah daga Ebonyi, a matsayin ƙaramin ministan lafiya, da Odum Udi daga Rivers a matsayin ƙaramin ministan muhalli, da Ademola Adewole Adegoroye daga Ondo a matsayin ƙaramin ministan suuri.

Shugaban ya taya su murna, tare da buƙatar su yi aiki tuƙuru don ciyar da ƙasar gaba.

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post