WWCU20: Najeriya ta tsallake zuwa zagayen kwata final na gasar cin kofin duniya ta mata 'yan kasa da shekaru 20

 Falconet
Kungiyar kwallon kafa ta mata na kasa da shekaru ashirin ta Nigeria ta lallasa kasa Korea da ci 1 da nema wanda Esther ONYENEZIDE ta saka kwallon a raga a minti 83 da taimakon OKWUCHUKWU.

Idan za a iya tunawa, a satin da ya gabata ne Falconet suka lallasa takwarar su ta kasar Faransa da ci daya da nema wanda hakan ya basu daman yin nasara har sau biyu a matakin rukuni.

A rukunin C, Nageriya ita ta daya da maki 6, sai Korea da ta ke biye ma Nijeriya da maki 3 sai kuma Faransa da Canada Wanda basu da maki ko daya inda suke matakin na 3 da na 4.

Najeriya dai za su kara da takwarar su ta kasar Canada ne a wasan karshe na rukuni daga bisani sai wasan mataki na gaba

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post