Daudar Gora Book 2 page 67

 

Daudar Gora Book 2 page 67

DAUDAR GORA 

Book 2

67

…. Suna barin sashen cikin tashin hankali tashige ciki tai kiranye uwa. Cikin kankanin lokaci kuwa sai gata ta bayyana alamar dama a kusa take. Ido rufe Malikat Bushirat ta zayyanema uwa duk abinda ya faru tsakaninta da Iffah. Yanda uwa ke huci sai ya koma tsorata Malikat Bushirat din, tuni nata fushin da harzukar suka bace. Zabura tai gefe jin sautin kakkausar muryar uwa mai tsananin amo acikin

kunnenta.

   "Wannan fadan ba naki bane damu takeyi!!! Lallai damu takeyi. Ita wacece? Yar wacece? Mitake takama da shi?! Zan tabbatar da ba uwarta kawai ba, hatta dukkan ahalinta sai sunyi nadama da dana sanin kasancewarta jininsu!!!!. Wanda suka fitama sunja bata kai musu ba balle ita haihuwar jiya-jiya.".


  Ta fada cikin wani irin karaji da dukan kasa da tafin hanunta, tare da rantsuwa da wani kasurgumin gunkin da take bautawa wanda sam Malikat Bushirat ita bama ta fahimta ba. Ji Malikat Bushirat din tai hatta dakin girgizawa yake, tamkar tashin guguwa uwa ta bace bat a dakin. Wani irin numfashi ta sauke mai nauyi, tare da zama jagwaf. Ta jima numfashinta na kai komo kafin ta samu daidatonsa, sai kuma ta saki murmushi mai matukar kayatarwa da dan tabe baki ta dage kamafada irin ko'a jikinta din nan,wanna kuma fadan yimata shi za'ai.

Ni dai nace, "Humm" 🥱😂🚴

. WASHE GARI.    

Kasancewar ba' a ga wata a jyan ba basu wuce ba. Hakan sai ya saka Iffah yini a sashen Malikat Haseenat. Sai bayan sallar la'asar ta dawo. Lokacin su Tajwar Eshaan da was manyan masarautar na'a can saman ginin da agogon da duk ta inda ka bullo ta birnin Dahab City din zaka gansa da na'urorin ganin wata, Cikin amincewar UBANGIJI kuwa sai gashi an gansa, Dan danan kafofin yada labarai suka fara sanarwa da yawn Shahan-shan, dan shi da kansa yake duban wata tun hawansa mulki babu wani wakili.

    Alhamdullah washe gari an wayi gar da azumin watan Ramadan a bakunan mutane. Yayinda jirgin Tajwar Eshaan da Iffah sai hadimai hudu mata shida maza. A ciki akwai hadiman sashen Malikat Haseenat da Iffah ta roka ta bata su su biyu har da hadima Banou. Lokacin da akace mata zatabi Iffah rikicewa tai harda kukanta a boye. Sal Diwa amintacciyar hadimar Malikat Bushirat ta zahri, wadda itama dai Iffah!r ce ta nema ta bata a gaban Tajwar Eshaar babu yanda ta ya ta bata, sai hiyu da suka kasance daya a cikinsu hadimar da Uwa tace zasu batane samun wanna damar yasa suka cusata a ciki.Tafiyace ta sirri dan haka babu wanda yasan da ita a Kasar, ko'a cikin masarautar a ba kowa ya san da Shahan-shan din za'ai ba. Kowa ya dauka Iffah'r ce kawai zatai gaba kafin su Malikat Haseenat da ake hasashen kila sue su samesu acan tunda suma sukanje duk kusan bayan shekara uku, tun bayan hawan Tajwar Eshaan din kuma sau daya sukaje,shiko tunda ya hau mulkin ma bai taba ma zuwa ba sai yanzu.

    Lokacin da jirgi ke barin kasa wani irin kudindinewa Iffah tai a jikinsa na toro. Ta bashi dariya dan ya fahimci duk irin abubuwan nan tsoronsu takeji. Ga Elevator ma in zata shiga yanda take kasancewa balle kuma anan, tafa gwammace tabi stairs duk wahalarsa idan ita kadai ce. Rungure kayarsa yay dan su kadai ne, hadiman na nasu sashe daban. Koda jirgin ya gama dai-daita bata bar jikin nasa ba: sai ma barci da yay awan gaba da ita mai nauyi. Ajiyar zuciya ya saki yana mai sumbatar idanunta. Azuciyarsa ya ce, (Fitinanniyar yarinya nima nadan huta da surutunki) a zahiri kam sai ya gyara mata kwanciya nutsuwa na sake saukar masa. Shi kadai yasan kaunar da yakema yarinyar nan, ALLAH dai yasa karta zama ajalinsa.

😂Oh oh masoyan asali. 😉

SAUDI ARABIA

Mamaki hade da al'ajabi ne ya mamaye Iffah lokacin da suke fita a cikin jirgin hannunta cikin nasa. Wasu zuka-zukan motocine na alfarma da tawagar masarautar Saudiya, yayinda Sultan a Saudiyya ne da kansa yazo tarbar Tajwar Eshaan ibn Haysam Abdul-majeed Ally Qutb ba sako ba. Cikin farin ciki sarakunan biyu masu karfin fada aji a duniyar musulinci suka tarbi juna. Sam Tajwar Eshaan bai saki hannun Iffah ba har suka rungume juna da Sultan din. Bayan sun saki junan ne ta dan rissinar da kanta alamar girmamawa ga Sultan din.Fuskarsa kawance da murmushi yay mata kallo daya da musulunci ya shardanta ya dauke kansa. Ya fai mata barka da zuwa DAULAR MUSULUNCI cike da mutuntawa a gareta duk da yasan zai iya haihuwarta. Dan manyan yaranta maza twins guda biyu suma bazasu wuce 20years ba karnar Iffah'r..

A hankali ta sauke ajiyar zuciya tana lumshe idanunta jin sanyin ac da kamshi mai shegen dadi ya ratsa hancinta lokacin da suke shiga daya daga cikin manyan motocin da sukazo tarbarsu. Dubanta Tajwar Eshaan yay tare da rungumota jikinsa da kyau. Tako late kamar yar mage tana shakar daddadan kamshinsa. Ashe Iffah ba komai ta gani a airport din nan ba. Sai da suka shiga babbar daular da lissafin dukiyar cikinta ma da kawatuwa bata lokacine. Tabbas tasan Daular ruman ta had, irin haduwar da babu wanda zai shiga bai yi santi ba. A tunaninta da anya akwai makamanciyar irin daularsu a duniya? Amma a yau ta tabbatar akwai, dan duk da daular Saudiyya bazatafi tasu ba, suma tasu bazata fita ba, dan nan clin ma dai badaga baya ba Dan in za'a baka zabima zaka ya kasa banbancewa ne tsabar shiga

rudani.

    An musu tarba ta mutuntawa da tsantsar girmamawa, tare da masauki dan gaske da ko'a kasarsu iya abinda zasu iyama kansu kenan. Tattare suke da gajiya, musamman I/fah daba sabawa tai ba ga kuma azumi, saukin ma farkon farawa ne. Da kyar ya lallabata tal dan wanka ta kwanta. Kafin kace mi barci yay awan gaba da ita.

    Bata samu kanta ba sai la'asar, shima da kyar ya tadata sanda zai wuce massalaci. Bayan ya dawo yace ta shirya zasu wuce madina ne da ansha ruwa, da ga haka ya fice ita kuma wasu mata sukazo mata da kaya inji matar sultan. Sun jirata ta shirya sukai mata jagoranci zuwa sashen matar sultan din, inda ta samu tarba ta mutuntawa da har ta dinga jin kanta ya kara girma itama a yau. Dan duk da matar sultan din ta girmeta sosai janta ta dinga yi a jikinta cike da kulawa harda cewa itafa tana so ta saki likinta da ita ne dan sun zama kawaye. Murmushi kawai Iffah tayi mai sanyi. Ta wani nutsu kamar ba Iffah'r nan mai shegen surutu ba mai addabar Tajwar Eshaan. Magana ma an koma amsata ne dai-dai cikin nutsuwa da kamewa ita a dole ga matar Shahan-shan na kasar ruman (Ashe akwai a inda bakin Iffah zai mutu haka (😂). Suna a tare har aka sha ruwa, a tare suka gabatar da sallar magrib sannan suka fito kayataccen falo karami na musamman da aka shirya musu kayan alatu na shan ruwa. Daga ita sai uwargidan Sultan da Shahan-shan din ta. Sai wani irin binta da kallon nan nasa na kasan ido yake kamar zai hadiyeta dan ta masa matukar kyau cikin kykyawar bakar abayar data haske farar fatarta ga walwalin fararen duwatsu da akai mata ado dasu. Itama dai uwargidan Sultan irin kayanne a jikinta. Haka shima da Sultan din kayansu iri gudane. Lallausar farar jallabiya mai tsadar gaske an daura bakar alkyabba da akaima adon golden da mayafi fari tas a saman kawunansu. Kamshi dai nasa ne, dan daga su sai turarrukansu sukazo kasar. An sake gaisuwa irin ta manyan attajirai masu mulki da karfin iko, sannan a nutse sukai buda baki mai sauki (ba irin na su bily ba da sai anji ciki yay nak babugurin tura kosai 🥱), Karancin lokaci ya saka sarakunan biyu mikewa zuwa gabatar da sallar isha'i. Suma kuma su Iffah suka kora bedroom din uwarg/klan Sultah suka gabatar da tasu. Suna idarwa basu zauna ba, dan tafiya tsakanin nan da Madina akwai nisan gaske, dan ma lafiyayyun motocine. Sai lokacin Iffah ta san ashe tare da Sultan din da matar tasa ma zasu wuce. Tofa wayaga in da ranka kasha kallo, dan kuwa dal acikin zukekiyar motar da zasuyi tafiyarma dai an shirya musu abincine, ga an shiryar motar daga aiki kamar wani daki ha musamman. Iffah dai da al'amarin ya zame mata sabo ga kauyanci ga son nuna class t3, haka mutunivar tamu akaita basarwa kamar komai ba komai dai kun gane ai 😉(Kuka yarda naje gurin nan alkur'an sai na nuna hali, dan kowa sai yasan Bilyn Abdull daga 9ja nazo 🤣😆🚴).

     A yanzun kam sarakunan biyu sun baje filin hirarsu a nutse ga matansu a gefensu. Har takai ita dai Iffah ta fara ma hamma. Cikin mamaki Tajwar Eshaan yake mata kalion nan nasa na kasan ido, dan ya fara sakama yawn barcin nan nata alamar tambaya. Abu kadan ta fara hamma, yanzu zata tashi anjima kadan ta sake kwanci. Kuma bazaka taba ji tace barcin yaisheta ba. Anya kuwa? (Sa a bincika mana mai rumawaja🚴).


* MADINA BABBAN BIRNI BURIN ZUWAN DUK WANI MUSULMIL*

Duk da dare yayi kai tsaye massalacin MANZON ALLAH (S.A.W) suka wuce, inda nan ma suka samu tarbar da ga shugaban garin na Madina da tawagarsa cikin girmamawa ga Sultan din nasu a Saudiya gaba daya da kuma babban bakonsa shugaban kasar ruman. sai da suka gabatar da salla raka'a biyu sannan sukai zaman jira karasawar lokacin asubahi Basu bar mascalacin ba sal bayan sallar asuba. Yanzun ma dai wani katafaran gida aka kaisu. Gida daya amsa sunansa gida bawai muna gida ba. Gajiyar da ke tattare da kowa yasa ruwa kawai suka watsa kowa ya kwanta musamman ma Iffah dake jin kamar zatayi adungure tun a massalaci…..✍️

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post