Kurkukun Ƙaddara Book 2 Page 33

 


~*✊💋BossLadiesWriters💋✊*~_

          سجن القدر❤

*2 pages ne a hade, dama na faɗa maku 4 days zan koma yin update a week, tomorrow zanyi amfani, till jibi zaku samu next page✍️

*WAIWAYE ADON TAFIYA💫*

(Abunda ya faru bayan zahra ta faɗa ma Aneelerh halin da take aciki, Na kuɗi da hajiya falmata take binta bashi, bayan ta koma ɗaki damuwa ta isheta, tayi ƙarfin haline kawai wurin bata shawara akan ta amince da buƙatar hajiya falmata saboda tana son ta jaraba zahra ne don taga idan tana da hankali, tunani ta soma yi ta wace hanya zata Iya taimakonta? Nan take zuciyarta ta bata shawarar tayi amfani da sauran kuɗin nan da jami'an sirri suka bata, har yau bata ƙarar dasu ba, tamkar tana jin tsoron ta6a su, tun dai data siya ma baby junaid kayan wasa bata ƙara cirar ko naira biyar ba.


Ba tare da sanin kowa ba Aneelerh ta tuntu6i mahboob, a ɗakin shi ta same shi, ta tambaye shi koya san gidan hajiya falmata mahaifiyar ƙawar zahra? Yace mata eh yasan gidan, sun ta6a zuwa tare da zahran ma, tace toh so nake ka rakani gidan, da mamaki akan fuskarshi yace amma me zakiyi acan din kinsan ta ne? girgiza mashi kai tay alamar a'a, kawai inaso ka rakani muje, idan mun fita zan faɗa maka komai, amma kafin muje gidan zaka fara rakani banki, akwai wasu kuɗi da nakeson in cira, Jin ta ambaci kuɗi yasa mahboob saurin amincewa zai kaita gidan, a cikin motarshi ya dauki aneeleeh saida suka fara biyawa banki ta ciri kuɗin kafin suka nufi gidan hajiya falmata.


  Lokacin da suka karasa gidan, A parking space mahboob Ya tsayar da motar, Aneelerh tace dashi ya jirata anan, ya amsa mata da toh, da sallama abakinta ta shiga palourn gidan, adai dai lokacin mai aikin gidan ta fito daga kitchen ta yi arba da aneelerh, fuskarta da fara'a suka gaisa tace mata wurin hajiya falmata tazo, Allah yasa tana nan, Mai aikin tace bata jima da dawowa daga office ba, ki zauna bari naje in sanar da ita, da sauri mai aikin taje ta fado mata, jim kadan ta dawo ta sanar da aneelerh sakon hajiya tace ta jirata gata nan zuwa, aneelerh ta amsa mata da toh, kusan mintuna biyar Aneelerh tana a tsaye ta ruƙe qugu tana jiran fitowarta, cikin jin fargabar ganin matar, sai faman bin palourn take yi da kallo.


 Sautin takun tafiyarta ne Yaja hankalin Aneeleerh ga kallonta, A hankali take saukowa down stair, ta ɗauki wankan tsadaddan leshi, kanta yasha ɗaurin ɗan kwali, ta manna farin glass a idonta, Babbar macace tana da jiki, tana tafiya tsokokin jikinta na motsawa, Fatar jikinta tasha hutu har ta gaji, daga ganin fuskarta masifaffiyace, idanuwanta mitsi mitsi da su kamar na mutanan Yankin china, hancinta kuwa abaje yake, ga big mouth dinta yasha man baki.


  Ta6e baki Aneeleerh tayi aranta ta furta jibarta dan Allah, ƙatuwar banza da ita kamar buhun masara, a haka take lalata rayuwar matasan ƴan mata, Allah dai ya shirya, wasu mutanan sunyi asarar rayuwarsu.


 Lokacin da hajiya falmata ta ƙarasa saukowa daga saman benan, idanuwanta suka Yi mata tozali da kyakkyawar fuskar Aneelerh nan take taji ta burgeta, tayi mamakin ganin baƙuwar fuska agidanta, bakomai yafi tafiya da imaninta ba face Kyawun surar Aneelerh.


  Ganin Yadda Ta tsareta da idone Yasa Aneelerh tayi saurin gyara mayafinta ta rurrufe jikinta, Aranta ta furta A'uzubillahi minasshaidanirrajin, Aniyarki ta biki baƙar mayya"

 Saman sofa din dake fuskantar Aneelerh Hajiya ta zauna, tana dubanta da wani irin mayataccen kallo.


 Yamutsa fuska Aneelerh tayi fuskarta ba wasa tace"barka da Yamma"

 Hajiya falmata ta amsa mata da"barka dai, bismillah ki zauna mana"


 Ɗaure fuska Aneela tayi"bana zama agidan da ake aikata sa6on Allah, saboda ni tsarkakakkiya ce, bai kamata in goga ma jikina najasa ba"!! Mamakine Ya kama hajiya falmata, a hankali ta sauke glass din dake saman fuskarta don ta samu damar ƙarewa Aneelerh kallo.


  "Bansan wacece ke ba, sai dai na fahimci haukan talauci ne ke damunki shiyasa kika kwaso ƙafa kika zo gidana don in taimaka maki"


 Dariyar rainin wayau Aneelarh Tayi kafin tace"ki kalleni daga ƙasa har sama, kema kinsan nafi ƙarfin ki kira ni da talauci, Ni banzo don nayi cece kuce dake ba saboda bani da lokacinki, Maganar kudin zahra da kike bin ta bashi ne"

 Shu'umin murmushi ne Ya bayyana akan fuskar Hajiya falmata da shaƙiyanci ta furta"oh, kinzo ne ki fanshe ta, shiyasa kika kawo min kanki? Donni banga alamun zaki Iya biyan kuɗin ba"

  Girgiza kai Aneelerh tayi ranta a6ace tace"wato shi dai jaki duk yadda akai dashi sai yaci kara, idan kina tunanin na kawo maki kaina ne don in fanshi zarah to ki daina, domin kuwa nafi ƙarfin ƙasƙantacciyar mace ballagaza jahila kuma daƙiƙiya irinki, Mace mara tsoron Allah, me yin amfani da dukiyarta don lalata rayuwar matasan ƴan mata masu neman nakansu, Wlh kinji haushin rayuwar......" gigitacciyar tsawa Hajiya falmata ta daka ma Aneelerh, tamkar damusa ta yunƙura ta miƙe tsaye tana duban Aneelerh da mummunar fuskarta babu annuri ko misƙala zarratin ta nuna mata Hanyar fita da yatsan hannunta"Ke Fuce kibar min gidana, tunkafin ranki Ya 6aci, matsiyaciyar banza masu ƙashin tsiya"


 Aneelerh da ƙarfin Hali tace"idan kinga na fita gidan nan to nagama faɗin ta cikina ne, Kuma wallahi koda gigin wasa kika ce zaki ta6a lafiyar jikina saina naƙasa ki bakisan wacece Ni ba" ta faɗa tana jefa mata harara, lamarin Ya ɗaurewa Hajiya falmata kai, ganin karfin hali na Yarinyar nan data zo gidanta tana Yi mata rashin Kunya.

 Goya hannayenta tayi saman ƙirjinta"ina sauraronki, Me ya kawo ki gidana!"

 Gyaɗa Kai Aneelerh Tayi"zuwa nayi don Inyi maki nasiha, don na fahimci Wadda iyayenki suka yi maki tuni shaiɗan Ya hure maki kunne, dan Allah Jibarki cikin shiga ta mutunci kamar wata mutuniyar arziƙi, al'halin nan kuwa fuska biyuce ke, A fili musa a zuciya fir'auna, Haba baiwar Allah, Da hankalinki da tunaninki da shekarunki kika za6i ki sa6awa Allah don kawai ki ji daɗin duniya? Kin manta da Allah yana ganinki kuma zaki mutu ki koma gareshi, a ko'wani yanayi mutuwa tana iya riskarki, idan taƙamarki kuɗine ki tuna Allah ne Ya baki Arziƙin bake kikayi ma kanki ba, Idan yaso zai Iya ƙwace wa, kuɗi da kike gani wallahi masifane Idan baka tafiyar dasu ta hanyar da ta dace ba, Ita kuma rayuwar duniya jin daɗinta ƙalilan nan bata da tabbas, bakisan yaushe zaki mutu ba, kin sanya mugunta aranki saboda Allah Ya azurtaki, Kina cutar matasan Ƴan mata, waɗanda Iyayen su suka sha wahalar basu tarbiya ke kuma kina gur6ata masu rayuwarsu, Allah kaɗai yasan adadin Ƴan matan da kika 6ata, kin goga masu jarabar da bazasu Iya gogeta ba, Kin cutar da rayuwarsu mutane suna kuka da su saboda sun addabi rayuwar al'umma kuma ire-iren ku ne ku ka yi silar lalacewarsu, wallahi kiji tsoron Allah kamar yarda ba zaki so ayi da ƴar ki ba to kema kada Kiyi da ɗan wani, duk da naji irinku Harda ƴa'ƴan naku kuke Yi, saboda shafewar basira da neman duniya kun makance bakwaji bakwa gani ku ala dole saikun siyama kanku tikitin shiga wuta"? Tun da Aneelerh ta soma Yi mata magana da faɗa haɗi da tsiwa take ta faman zare ido tana binta da kallo, tun da take arayuwarta wani ɗan adam bai ta6a gigin tunkararta Ya faɗa mata magana game da abunda Take aikatawa ba sai Yau da Allah Ya haɗa ta da Auntyn Zahra mai dimple, Ayoyin kur'ani aneelerh ta soma karanto mata tana fassara mata, kamar an rufe mata baki takasa dakatar da ita duk irin masifar da take da ita yau an kashe mata bakinta

 "Allah Yana son bayinshi waɗanda suka aikata 6arna suka tu6a saboda tsoronshi suka koma gareshi, dan Haka ina baki shawarar tunkafin lokaci Ya qure maki Hajiya falmata ki Gyara Halayanki, Ni bance zan sanyaki ki shiryu ba don nasan irinku taurin kaine daku kamar kwakwa, ko malamai sunyi maku nasiha bakwaji bakwa gani sai ranar da Allah Ya damƙe ku tukunna zaku gane kurenku, Ni in banda ma shafewar basira, wai ku bakwa tuna mutuwa da kwanciyar ƙabari ne? Baku tuna duk abunda kuka mallaka zai ƙare, daga kai sai halinka za'a binne ka a ƙabarin ka fa? Ke yanzu kin za6i ki mutu kina aikata mummunan zunubi na bin Ƴan uwanki mata? Ga hakkin Iyayen da kika sanyasu zubar da hawayensu ta silar lalata masu rayuwar ƴa'ƴa da ki ka yi ga kuma Matasan ƴan matan da kika gur6ata ma rayuwa, wannan fa zunubine mai cigaba da yaɗuwa ko bayan kin mutu zaki cigaba da samun kamasho acikin shi, saboda kinbar tarin ƴan matan da kika gur6ata agari suna aikata fasadi, wallahi kiji tsoron Allah tunkafin lokaci Ya qure maki, Ina ƙara jan hankalinki ki tuba ki koma ga Allah tunkan mutuwa ta risƙe ki don ita bata kwankwasama mutun ƙofa balle Yace zai shirya mata"


 Wata irin zuface ta soma wanke goshin Hajiya falmata, Haƙiƙa kalaman Aneelerh sun fara karya mata zuciya, sai faman zare ido take Yi, batasan ya akai ta tsinci kanta da jin maganar Aneeleerh ba, Yarinyar tayi matuƙar burgeta kuma ta bata mamaki da har ta iya yi mata nasiha batare da jin shakkarta ba, saboda mutane dayawa basa Iya yin magana agabanta, amma Ita wannan ido cikin ido take furta mata magana .


 "hajiya falmata, duk runtsi duk wuya kada ki Karya zuciyar wanda Ya aminta dake! Ina magana akan zahra da ta dauke ki tamkar mahaifiyarta saboda ƙaunar dake a tsakaninta da ƴarki fatima, Kin karya mata zuciya, naji daci lokacin da na sameta ta kulle kanta acikin toilet tana Yin kuka babu ci babu sha ita kaɗai batare da kowa ya sani ba, Kin hanata runtsawa saboda taƙi baki haɗin kai ku aikata sa6on Allah, haba baiwar Allah, idan kece akayima yarki haka zakiji daɗi! Don kawai mutun Na buƙatar agazawarka sai kayi anfani da dukiyarka donka cutar dashi? Babu wanda yafi ƙarfin ya nemi taimako a duniyar nan, koda ba a wurin mutun ɗan uwansa ba, zai nema awurin Allah  Idan har baka agazama bawansa ba tayaya kake tunanin zai agaza maka? 


Jinjina kai Aneelerh tayi, Tuni zafafan hawaye sun wanke fuskarta cikin muryar kuka taci gaba da cewa"Kin ƙona mata rai, zahra ta yarda dake fiye da tsammaninki, tana kuka tana fadamin yadda ta aminta dake amma kika karya mata zuciya, Zahra da kike gani tafi ki Hankali, Yarinyar tana da tawakkali, tana jin tsoron Allah, Na jarabata don inga ko tana da wayon jure ƙaddara idan ta sameta, Ni dakaina nabata shawarar ta baki haɗin kai, da buɗar bakinta sai ce mun tayi ita ko duniya za'a mallaka mata bazata ta6a amincewa ta sa6ama Allah ba, saboda tana jin tsoron shi kuma tana jin tsoron ranar da zata koma gare shi, Hajiya falmata kin ta6a tunanin hakan? A matsayinki na babbar mace wadda ta haura shekara arba'in da ɗuriya a duniya? Shekaru sunja amma baki tsoron mahaliccin ki? Kina amfani da dukiyarki wurin Gur6ata duniyarki da lahirarki, maimakon kiyi amfani da su wurin taimakon bayin Allah marasa ƙarfi wadanda zasuyi alfahari dake ko bayan ba ranki kuma ki samu lada awurin Allah, Yanzu ina amfanin irin wannan rayuwar da kika daukarwa kanki"!?


  Ƙafafuwanta ne suka gaza ruƙeta, Jiri Ta soma gani a cikin idanuwanta, adaddafe ta nufi sofa ta zauna tana faman fitar da numfashi.


  Hankaɗe Kafaɗa Aneeleerh Tayi"Alhamdulillah nagama faɗar ta cikina, duk wanda yayi da kyau don kanshi, akwai mutuwa akwai hisabi, maganar kuɗi Kuma nazo maki da su miliyan Uku Cuf, Idan ma kina son ƙari zan ƙara maki, saboda inaso kisan muba jinin faƙirai bane idan arziƙine muma mun gaje shi gaba da Baya" 


Ɗaga murya Aneelerh Tayi da ƙarfi ta furta sunan Mahboob, shigowa ɗakin Yayi hannun shi ruƙe da jaka baƙa, tunkan ya ƙarasa yake bin ko'ina da kallo, ganin haɗuwar falon gidan aranshi Ya ayyana Lallai hajiyar nan ta tara shiyasa take tsula tsiyarta son ranta saboda tana da arziƙi.


  "Zoka ajiye mata tsiyarta," Aneelerh ta faɗa tana nuna mashi gaban Hajiya falmata, Ta zabga uban tagumi da hannu biyu, da alamun nadama atattare da ita.


 Koda mahboob Yayi arba da fuskarta saida yasha jinin jikin shi ganin yadda ta haɗe rai, ga gumi na fita a goshinta.


  Kamar mai jin tsoronta Haka Ya ajiye mata jakar agabanta.


  Aneelerh ta ruƙo hannun shi acikin nata, har sun ɗaga ƙafa zasu bar falon muryar Hajiya falmata ta dakatar da su

  "Dan Allah Ku tsaya"!! Kusan atare zuciyarsu ta buga, a sukwane suka waiwayo suna dubanta, Gabansu ba ƙaramin faɗuwa yayi ba ganin ta fashe da kuka, miƙewa tayi daga saman sofa din ta nufe su tana fadin"wallahi nayi nadama, dan Allah kuyi haƙuri da abun kunyar dana aikata, Nima ba halina bane ƙawayene suka tunzurani har na faɗa harkar" zubewa tayi saman gwiwowinta agaban aneelerh tana kuka tace"Tun da nake a rayuwata wani ɗan adam bai ta6a yi mini nasihar data ratsa zuciyata ba sai akanki, bansan wacece ke ba, amma nayi sha'awar In yi koyi da kyawawan  halayanki, duk naji na tsani kaina, na zubda mutuncina da girmana a idon zahra, wallahi naji kunyar da ban ta6a jin taba, Naji ƙuncin Halin dana jefa zahra, saboda ni tagaza runtsawa Na hana baiwar Allah yin bacci na hanata cin abinci, na jefa rayuwarta cikin ƙunci batare da nayi tunanin raɗaɗin da zataji acikin Zuciyarta ba, wallahi nayi nadama koda ace bazaku yarda dani ba, Na tuba kuma in sha Allah bazan ƙara aikata zunubin nan ba, angama bi'iznilillahi, saboda inaso Inyi kyakkyawan ƙarshe kuma inaso in tsira ranar gobe ƙiyama, In sha Allah daga yanzu nagama yin amfani da dukiyata don in sa6awa Allah, da kuma gur6ata tarbiyar ya'yan mutane....."daƙyar ta ƙare maganar tana faman jan magina.


  Ba Aneelerh ba hatta Mahboob Yayi mamakin wannan Ikon Allahn, sun yi sototo suna kallonta kamar sakarkaru duk ta zama abun tausayi tsoron Allah ya shigeta, wata'ƙil dama itace silar shiriyarta shiyasa Allah Ya haɗasu da ita.


  Muryar Hajiya falmata na rawa tace"Ku taimaka mun dan Allah, inason in wanke kaina awurin zahra, saboda inason taci gaba da kallona kamar yarda tasanni ada, Nayi alƙawarin zan taimakamata, kuɗin da ku ka zo dasu na yafe mata ku ɗauka ku maida mata su, Sannan inaso taci gaba da yin aiki a company dina, Kayan da suke son ayi masu order A dubai gobe in sha Allah zasu iso Nigeria"


  Kallon juna mahboob da Aneelerh suka ƙara Yi, Atare suka furta Alhamdulillah, Aneelerh tace"nagode ma Allah daya bani baiwar Iya tsara kalamin da har suka ja hankalinki, Naji daɗi dana zama silar shiriyarki, Ina fata zaki canza rayuwarki daga Yau ki koma ta gari, wadda kowa zaiyi alfahari da ita"


 Jinjina kai Hajiya falmata tayi Cikin sanyin murya tace"in sha Allah," ruƙo hannayenta aneelerh tayi acikin nata, miƙewa tayi tsaye suna fuskantar juna

 "Ki godema Allah, saboda Yana son ki da shiriya shiyasa Ya baki damar gyara rayuwarki tun da sauran numfashinki,"


  Jinina Kai Hajiya falmata tayi.

 Aneeleerh ta ƙara da cewa"sai dai kiyi haƙuri, ba zamu maida kuɗinba, nariga dana kawo maki dasu, Ki ruƙe su a hannunki, zahra kuma bazata ƙara Yin aiki a companynku ba, zan nema mata aiki awani wurin"!! 


  Magiya hajiya falmata tadinga yi mata akan tayi haƙuri su koma da kuɗin, ta yafe masu, amma Aneelerh taƙi yarda, mahboob ne yace ta jira zasu yanke shawara a tsakaninsu, ruƙo hannun Aneelerh yai acikin nashi yajata zuwa gefe ɗaya akwai tazara tsakaninsu da hajiya falmata, tayi kasake tana kallonsu

  "Aunty aneelerh tunda tace ta yafe kuɗin mu koma dasu kawai, ai ba roƙonta mukayi ba"

 Girgiza kai aneelerh tayi"nidai hankalina bai kwanta da matar ba, wallahi irinsu shaiɗanune Mahboob, inajin tsoron ace wani tuggun zata kitsa mana shiyasa tace ta yafe kuɗin, ƙwara mu maida mata aniyarta"

  Yamutsa fuska mahboob yai"aunty aneelerh just ki gane, ni dai na yarda da ita, sau dayawa zaki ga mutun yana aikata ba daidai ba idan Allah yaso shi da rahama saiki ga ya shiryu cikin sauƙi batare da ansha wahala ba, Yanzu ki duba matar can, hada fa kukanta kuma har zuƙunnawa tayi saman gwiwowinta tana roƙonmu, why bazamu yafe mata ba? Komai ya wuce, ita kanta zahran ba ƙaramin daɗi zataji ba saboda tana son fatima ƴarta aminnan junane tun tuni, sannan taci burin zuwa obie estate, bayan haka aikin nan da take Yi a companyn su ba ƙaramin ƙaruwa take Yi ba, ita kanta tana faɗi da bakinta irin alheran da take samu ta silar aikin da suke Yima mutane, idan ma da wata manufa tace hakan to mu barta da Allah, In sha Allah babu abunda zata Iya yi mata," gyaɗa kai Aneelerh tayi"shikenan na amince da buƙatarta, mu koma mu faɗa mata" komawa sukayi cikin falon, bayan sun sanar da ita shawarar da suka Yanke ta dinga yi masu godiya farin ciki duk Ya cikata, kafin tafiyarsu saida ta roƙe su alfarma akan su taimaka mata, tana so zahra taci gaba da ganinta a matsayin mahafiyarta, tasan ayanzu bata da sauran mutunci a idonta.

 Aneelerh ce tabata shawarar yadda zata tsara ma zahra, duk don ta amince da cewa ba halinta bane, sun jima agidan kafin daga bisani sukayi mata sallama, sunyi rabuwar mutunci da hajiya falmata, har musayar number sukayi da Aneelerh saboda acigaba da zumunci.


  ( kunji abun da Ya faru, kafin washe garin ranar da zahra taje kaima Hajiya falmata kuɗinta)

  

Wuraren ƙarfe takwas na dare, motar drivern da yaje dauko su Alhaji ubaid daga airport ta kunno kai gate din gidan, tunkafin ƙarasowarsu, Dr Shureim da zeenatu suna atsaye bakin Entry hall din falo, hannunsu ruke cikin na juna, daga ita har shi jallabiyace ajikinsu, ta yafa mayafi akanta, tsantsar farin cikine akan fuskokinsu, sunyi matuƙar ƙagara da son ganinsu.

 Zeenatu sai faman washe baki take Yi, tunda tayi tozali da motar dake shigowa tana tunkaro bakin entry hall din 

  Da zamudi tace"ya shureim kana ganin aunty benazir zata Iya gane ni kuwa? Saboda mommy ta fadamin tun ina jaririya ta 6ace ba'a ganta ba" 

 Fuskarshi dauke da murmushi yace"idan ma bata gane ki ba, da zarar anyi mata bayani zata shaidaki, zan faɗa mata cewa zeenatu ce ɗiyar uncle musa, and my wife to be" tuntsirewa tayi da dariya taji daɗin maganarshi, muryarta da shagwa6a tace"amma ya shureim ai ni banaso ka faɗa mata, wallahi kunya nake ji, ko mommy layla ma kada ka fada mata please da daddyn ku" ta faɗa tana duban face dinshi.

  "Ai ni nafiso suji My zeenatu, saboda a fara shirye shiryen shafa fatihar auranmu" zaro mashi blue eyes dinta tai kafin tai saurin sanya tafukan hannayenta biyu ta rufe fuskarta cikin jin kunyar maganarshi ta furta"dan Allah yaya shureim dina kada ka fada masu yanzu, nidai kunya nake ji"


  "Kunya kamar bafullatana, kin manta mommynki baturiya ce, daddy musa kuma Hausa fulanine, kakarmu bafullatana ce kakan mu namiji kuma bahaushe ne, Ni bansan inda kika gado Kunyar nan taki ba, a haka zamuyi aure kina jin kunyata"?


  Kafin ta bashi amsa, motarsu Alhaji ubaid ta ƙaraso gab dasu, bayan drivern yai parking, da sauri Dr shureim Yaja hannun zeenatu suka ƙarasa bakin motar, yakai hannu ya buɗe masu murfin back seat, a hankali ta zuro da ƙafarta dake sanye cikin takalma, ƙarasa fitowa tayi tun daga ƙasa dr shureim yake binta da kallo, wankan atamfa ne a jikinta riga da skirt, ta kashe daurin dankwalinta, yalwatacciyar sumar kanta ta sauka gadon bayanta, gyalen asaman kafaɗa ta yafa shi, idan kaganta ahaka bazaka ta6a ce wa ta ta6a yin aure ba, kamar budurwa saboda babu abunda ya canza a jikinta, dama bata ta6a shayarwa ba.


  Wani irin kallon so da ƙaunar ƴan uwantaka suke jefa ma juna tsakanin ta da shureim, idanuwan kowannansu ya ciko tab da ƙwalla, La66anshi na kerma ya furta sunan ta"be.. Nazir! Yar uwata rabin raina, Jinin jikina Dagaske ke ce idanuwana suke nuna min? Fashewa tayi da matsanancin kuka, gaba ɗaya ta faɗa saman chest dinshi, ya zagayo da hannayenshi biyu ya rungumeta tamkar zai mayar da ita cikin cikinshi, Zeenatu dake tsaye tana kallonsu hawaye tuni sun wanke fuskarta, tsananin tausayin benazir ne Ya kamata, Fitowa Alhaji ubaid yai daga cikin motar shida Hajiya layla, ya dauki wankan shadda, itama layla Atamfar ce ta sanya sunyi anko da benazir hatta daurin dan kwalinsu da mayafin da ta daura a kafaɗa iri dayane dana benazir, idanuwansu na akan dr shureim da benazir, sun ƙanƙame juna sai kuka sukeyi kamar waɗanda suka rasa mafaɗi a duniya, zagayawa zeeenatu tayi ta 6angaren da su hajiya layla suke koda sukayi arba da ita, Hajiya layla ta buɗe mata hannu da fara'a akan fuskarta take fadin"Zonan My daughter zeenatu" kamar jira take yi da sauri ta ƙarasa ta faɗa jikin Layla, rungumeta tayi sosai, tana dan bubbuga bayanta ta furta"kin ƙara girma daughter, tsawon lokaci bamu haɗu ba, Daddynki Ya hanaki zumunci da ƴan uwanki, baison kina taka wajen mu, gashi mu kuma muna ƙaunarki" ta faɗa tana raba jikinta da na zeenatu, fuskokinsu dauke da annurin farin ciki, kallon Alhaji ubaid tai"sannunku da zuwa daddy" miƙa mata hannu yai da sauri ta ƙarasa gare shi, Yai hugging dinta yana fadin"fatan mun same ku lafiya," ɗagowa tai da kanta tana fadin"Lafiya lou daddy mu shiga daga ciki"

 Drivern daya daukosu Yana daga tsaye ya jingina bayanshi jikin motar, Yace"yalla6ai ku ƙarasa shiga gidan, za'a shigo maku da kayan naku" amsa mashi sukayi da toh, layla tace da su shureim ayi haƙuri adaina kukan ya isa haka mu shiga cikin gidan inyaso kun ƙare kukan naku acan" Alhaji ubaid na murmushi yace"ke ko kibarsu mana, An daɗe ba'a haɗu ba, Jini ɗaya ba wasa ba, mundai godema Allah daya bayyana mana ita da ranta da lafiyarta ubangiji Allah Ya ƙara tsare mana ita, layla da zeenatu suka amsa mashi da ameen,

 Gaba suka fara Yi, Ya rage saura zeenatu data ƙura ma benazir da shureim ido.


 Ta kwantar da kanta saman kafadarshi, yayin da hawaye masu ɗumi suke cigaba da wanke fuskarta, cikin muryar kuka take fadin"yaya shureim nayi danasanin duk wani abu daya faru arayuwata, wallahi nayi danasani mara amfani, bansan meke damunaba, hakanan na tafi nabar dangina nabar mijina, babban takaicina ƴar jinjirar dana bari cikin jini, na haura ƙafa na tafi nabarta saboda rashin hankali irin nawa, bansan meyasa na aikata hakan ba" cikin jin ƙunar rai ta ƙare maganar.

  Ɗaura hannunshi yai saman bayanta cikin rauni na murya ya soma magana"kiyi haƙuri benazir, wallahi ba laifinki bane, ni nasan duk rashin jin maganarki bazaki ta6a iya aikata hakan ba, Ina yi maki kyakkyawar zato, ki kwantar da hankalinki My sister" cikin kwantar da murya yake lallashinta

 Shessheƙar kukan zeenatu ne Ya janyo hankalinsu ga kallonta, idanuwanta sunyi luhu luhu, da mamaki akan fuskar benazir ta furta"yaya shureim a ina muka samu kyakkyawar matashiyar baturiya"?

 Fuskarshi dauke da murmushi yace"zeenatu ce, nasan ba lallai kisanta ba, saboda ba'ajima da haihuwarta ba ki ka tafi, ɗiyar uncle dinmu ce, ki kalli fuskarta dakyau"


  Farin cikine Ya lullu6e benazir, Yarinyar ta burgeta, Gata ƴar kyakkyawa da ita, miƙa mata hannu tai zonan ƴar uwata, Ina fata an fada maki wacece ni, idan ma ba'a sanar dake ba toh nidai sunana benazir, Ƙanwar dr.shureim" fashewa Zeenatu tayi da dariyar farin ciki, Hawaye nabin fuskarta.

"zonan In rungumeki ajikina, Nima yau inji ɗumin ƴar uwata" jiki Na rawa zeenatu ta nufi benazir suka rungume juna kamar zasu koma mutun ɗaya 

  Cikin shessheƙar kuka Zeenatu take fadin"Aunty benazir munyi kewarki sosai, Mommyna tana bani labarinki, najima ina son ganinki arayuwata, duk da bamu ta6a haɗuwa ba amma kullum idan nayi sallah sai nayi maki addu'a Akan Allah Ya bayyanar mana dake idan kina araye, Idan bakya araye Allah Yajiƙanki yakai rahama agareki, ashe da rabon zamu haɗu...."dakyar ta ƙare maganar saboda kukan daya cimmata, daga ita har benazir din kukan sukeyi, Kalaman zeenatu sunyi matuƙar ta6a mata zuciyata, tayi mamakin irin ƙaunar da take Yi mata, ita da bata ta6a ganinta ba, labarinta kaɗai aka bata, haƙika taji dadi mara misaltuwa, kaunar zeenatu ta shigeta, tayi fatan Ace itama ƴarta data bari tana yi mata addu'a.


  "Aunty benazir dan Allah kada ki ƙara tafiya kibarmu, wallahi muna kaunarki nida mommyna" sosai benazir ta fashe da kuka tana fadin"in sha Allah bazan ƙara tafiyaba, nadawo kenan zeenatu, naji dadin kalamanki agareni, ƴar uwata rabin raina"

  Dr.shureim Ya natsu yana kallonsu, idanuwanshi sun kaɗa jawur, hawayen dake gangarowa saman kuncinshi sai ƙara ninkuwa sukeyi.

  Cikin sanyin murya yace dasu'Mu shiga cikin gidan" amsa mashi sukayi da toh, hannun benazir acikin na zeenatu suka dunguma zuwa babban falon gidan.

  Lokacin da suka ƙarasa ciki, Alhaji ubaid da Hajiya layla suna a zaune saman sofa mai mazaunin mutun biyu, a yayin da Hajiya sarah ta zauna saman 3 sita, Alhaji musa yana daga zaune gefenta, kamar kullum fuskarshi babu annuri, kamar wanda akayiwa albishir da ranar mutuwarshi, shaddar jikinshi ta zauna mashi launin blue sky, daddadan kamshin turarenshi Ya karade hancin kowa, Hajiya sarah Lace ne ta sanya kalar shaddarshi, head dinta kalar takalman ƙafarta, sunyi kyau abunsu kamar sabbin ma'aurata


  Jin takun tafiyarsu yasa hajiya sarah ta ɗago tana dubansu, wani irin farin cikine ya lullu6eta ganin benazir, Jiki na rawa ta miƙe tana faman sakin fara'a fararen hakoranta tarr dasu ta nufi benazir tana fadin"ashe rai kanga rai? Benazir dagaske kece idanuwana suke nuna min? Wayyo Allahna, Idan ma mafarki nake Yi toh kada atadani abarni in tayi dan Allah" Rungume juna sukayi, Benazir ta fashe da wani sabon kukan bata ta6a tsammanin zata samu kyakkyawar tarba a wurin ahalinta ba, Tabbas sun bata mamaki tayi tunanin kamar yadda ta gudu babu wanda zai saurareta donta dawo gare su.

  Hajiya layla sai faman sakin murmushi take Yi ita da Alhaji ubaid hankalinsu na akan Hajiya sarah data rungume benazir, Shi kuwa Alhaji musa ko kallo bata ishe shi ba, tamkar baisan sun shigo falon ba.


  "Allah sarki benazir, Ashe da rabon zamu sake ganawa a duniyar nan! Tsawon shekaru sai yau Allah Ya nufa zan ƙara Yin tozali dake" ta fada tana duban benazir da hawaye suka gama wanke fuskarta

  Cikin shessheƙar kuka tace"Aunty Sarah nayi danasani, naji haushin kaina, naji na tsani kaina saboda komai ya faru arayuwana laifina ne, tunda nida kaina na gudu na tafi batare da nayi shawara da kowa ba, Dan Allah ku yafe min, nasan na 6ata maku rai"

  Idanuwan hajiya sarah tuni sun cicciko tab da ƙwalla, kasancewarta mace mai tausayi.

  Cikin karyayyar murya ta furta"dan Allah ki daina fadin hakan, Komai ya riga daya faru kuma ya wuce"


  Kafin benazir ta kuma yin magana muryar Alhaji musa ta katse masu hanzarinsu

  "Idan kun gama jimamin, ku ƙaraso ku zauna" cikin isa Ya furta hakan, sai lokacin Benazir ta ɗago da ido tana dubanshi, Ya haɗe rai babu annuri sam a fuskarshi, gani take kamar baiyi farin ciki da dawowarta ba.

  Ruƙo hannunta Hajiya sara tayi acikin nata, suka ƙarasa tare da samun wuri kowannansu ya zauna, zeenatu da dr shureim suna zaune saman lallausan carpet, Benazir kuma tana agefen hajiya sarah, ta ƙankame hannunta.

  A tsanake Alhaji musa Yasoma yin magana batare daya ɗago da ido ba

  "Da farko, Inayi maku barka da zuwa, yayana da kuma hajiya layla,' kwa6e fuska layla tayi aranta tace"dallah jibarshi ɗan rainin wayau"

  Numfasawa yai tamkar bayason buɗe baki Ya furta"benazir," amsa mashi tayi da na'am.

 Dawo nan ki zauna" yai maganar yana Nuna saman carpet daga gefen hannun sofa din da yake  zaune, jiki asanyaye ta miƙe ta dawo inda ya bata umarni ta zauna.

  Kowa ya natsu yana jiran jin me Alhaji musa zaice da ita.

  "Meyasa kika gudu daga gidan auranki har na tsawon shekaru baki nemi kowa ba"? Kafin benazir ta bashi amsa hajiya layla tayi saurin cewa"Bai kamata kayi mata wannan tambayar ba, kodai mu da muke Iyayenta bamu tambayeta komai ba, duba da halin da tadawo gidan"

 Ranshi a matuƙar 6ace ya dago da ido Yana binta da matsiyacin kallo batare daya furta komai ba

 Sai Alhaji ubaid ne yace"wannan maganar bata shafeki ba, tsakaninshi da ɗiyarshine don haka ki daina sanya masu baki" harara ta wurga ma Alhaji ubaid"kaima ka sani bazan ta6a rufe baki na ba, akan me zai tambayeta meyasa ta tafi? Lokacin da ta gudun ya nuna damuwane akanta? Ko kuwa ya bada gudummuwar da za'a nemota ne eye? Daga zuwanmu gidanshi zai tsareta da tambaya? Dama ya kira mune don Ya tuhumi ƴar mu badan Ya tayamu murnar ganinta ba" tunda tafara zazzaga masifa hankalin hajiya sarah dana zeenatu ya tashi haiƙam, shi kanshi shureim jikinshi yai sanyi laƙwas, benazir dai ta saddar da kanta ƙasa hawaye na cigaba da wanke fuskarta.


 Lallashinta Alhaji ubaid Ya soma Yi, Alhaji musa kuwa sai faman jinjina kanshi yake Yi, Yama rasa bakin magana


 Hajiya sarah na faman yarfa hannu tace"dan Allah kiyi haƙuri aunty, idan ranki ya 6aci, nasan ba'a kyauta ba, Ni tun farko banso yace kuzo nan ba, har magana nayi mashi akan mu yakamata mu taka muje tayaku murna amma ya hanamu zuwa...." daƙyar ta ƙare maganar ganin irin kallon da Alhaji musa ke binta dashi, ba arziƙi taja baki tayi shiru


Jinjina kai yaɗanyi kafin ya ɗaura da cewa"Allah Ya huci zuciyarki Hajiya layla, Naji bazan ƙara tambayarta ba," tayi mamakin jin abunda yace, har saida ta kalli cikin idonshi, murmushin gefen fuska yasakar mata afakaice, kafin Ya maida dubanshi ga benazir"ina yi maki barka da zuwa My daughter, naji daɗi da kika yi tunanin dawowa gida, ki kwantar da hankalinki, kuma ki share hawayenki, abunda ya faru ya riga daya wuce"

 Ajiyar zuciya benazir tadan sauke, cikin sanyin murya ta soma magana"nagode uncle, sannan idan na 6ata maka rai, kayi hakuri, nasan komai ya faru laifinane, dana kama hanya na tafi" 

 Lumshe idanuwanshi yadanyi kafin ya waresu akan fuskarta"kada ki damu ni ban ruƙe ki araina ba, kawai dai banji dadin guduwar da kikayi bane na tsawon shekaru batare da kin tuntu6emu ba, amma yanzu tunda kin dawo da ranki da lafiyarki falillahil hamdu, sai dai fatan Allah ya kyauta gaba, In sha Allah zanyi ƙoƙari dan ganin na inganta maki rayuwarki, duk wani abu da kike buƙata ki sanar dani zanyi maki shi, kada ki ƙara yunƙurin guduwa saboda muna buƙatarki, zaifi ki sanar damu idan ma wani abune ya 6ata maki rai a tsakaninmu zamu Iya sama maki solution, Ina fata kina jina"

  Ɗaga mashi kai tayi alamar eh, lamarin Alhaji musa ya ɗaurewa hajiya layla kai, bata ta6a tsammanin ya iya tsara kalami irin haka ba, hatta Alhaji ubaid yai mamakin yadda ya sakar ma benazir fuska yana yi mata magana cikin lallami, aranshi ya ayyana wata'ƙil tsananin tausayinta ne Ya kamashi, yaji dadin hakan, hankalin hajiya sarah ya kwanta dana zeenatu, sai faman sakin murmushi suke Yi, haka zalika dr.shureim shima murmushi ne akan fuskarshi.

   "In sha Allah uncle bazan ƙara yunkurin guduwa ba, duk runtsi duk wuya zan zauna atare daku, nima nayi danasanin abunda na aikata,

 Gyaɗa kanshi yai,

 Hajiya sara tace"tun ɗazu fa na sanya masu aiki sun shirya maku lafiyayyan abinci, yakamata muje muci kada ya huce" da fara"a akan face dinta ta furta hakan,

 Miƙewa sukayi atare suka dunguma zuwa dining room, benazir ta girgiza da ganin daular uncle musa, Gidan Ya tafi da imaninta.

  Saman dining chairs suka zazzauna, ga kayan abinci an jera masu saman table,"

  Tani da lami ne suka zo domin yin serving dinsu, Bayan sun gaishe da alhaji ubaid da hajiya layla, suka soma zuzzuba ma kowannansu abunda yake ra'ayin ci, hankalinsu kwance suke ci baka jin sautin komai saina ƙarar cokulansu.

  Jefi jefi zeenatu take satar kallon benazir da zarar sun haɗa ido sai ta sakar mata murmushi, Ta fahimci yarinyar ba ƙaramin so take Yi mata ba, Dr shureim na kallonsu, shima murmushine akan fuskarshi, Hajiya layla dai taƙi sakewa, itafa har yau har gobe bazata ta6a yadda da alhaji musa ba, gani take yi kamar akwai wata manufa atare dashi, abincin ma daƙyar take cin shi"


Bayan sun kammala cin abinci, Hajiya sarah ta rakasu zuwa masaukinsu da zasu zauna, Hadaddun bedrooms aka ware masu, Zeenatu ta hana benazir sakat, tsabar Iyayi hada ɗauko bargonta da pillow ta dawo down stair dakin benazir donsu dinga kwana atare, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi mata ba,


*SIR MUBARAK✊*


Yana acikin dangi suna ta yin firar yaushe rabo tare da Ƴan uwanshi, Wayarshi dake acikin aljihunshi ta soma Yin ruri, kusan sau uku kiran na shigowa yana yin rejecting batare daya ankare ba, saboda hayaniyar ƴan uwan shi da suke Yin fira a tsakaninsu, a babban katafaren falon gidan, a kira na huɗune, Senate lateef dake zaune gefenshi ya ankarar dashi ta hanyar yi mashi magana ka duba wayarka tun dazu nake jin sautin ringing ɗinta, amsa mashi yai da toh, sai da ya fara curo wayar ya duba sunan mai kiran nashi tukunna ya mike yai masu sallama Ya nufi ƙofar fita daga babban falon, bayan ya fitone Ya dakata da yin tafiya, Yabi kiran da aka yi mashi, bugu ɗaya aka ɗaga kiran

   "Major, ince dai lafiya? Naga miss call dinkane"

 On the other hand major yace"yalla6ai yaron nan na wurinka jazz Ya fita daga gida Yanzu haka da nakeyi maka magana munbiyo bayanshine muna asaman titi,"

  Cikin saurin murya sir mubarak yace"gani nan zuwa, kubi a hankali kada ku bari yaganku yaron wayau ne dashi, yanzu zamu biyo diddiginku" tunkafin maijor ya amsa mashi yai saurin yin rejecting call din, Ya dannawa driver dinshi Kira bugu ɗaya ya daga"Ina jiranka abakin entry hall na gidan baba, kazo da mota ka daukeni"

 Ya ƙare maganar tare da kashe kiran, Jikin shi har tsuma yake yi fatan shi Allah ya basu nasarar kama jazz don ganin menene yake aikatawa,

 Badajimawa ba baƙar mota ƙirar Range rover ta shararo da matsakaicin gudu bata nufi ko'ina ba sai bakin entry hall adai dai nan Tiger Yai parking dinta, Jiki na rawa sir mubarak Ya buɗe front seat na motar ya shige tare da bashi umarnin su tafi, reverse yai kafin ya karya kwana Ya nufi tanƙameman gate din fita daga estate din dake a kewaye da jami'ai, tunda suka hango sir mubarak ta tagar motar basu yi gigin dakatar dasu ba, kaitsaye motarsu ta haura saman titi, da gudun gaske tiger yake driving dinsu tamkar zasu tashi sama, sir mubarak yai amfani da phone dinsa wurin bin diddigin su major, cikin sa'a suka samo location din da suke, dare ne tamkar da rana saboda hasken street light daya gauraye ko'ina, hanyar da suka biyo kwata kwata babu mutane, sababbin gine gine ne a unguwar, wani ginin ma ba'a kammala shi.


  Rage gudun motar tiger yai ta hanyar glass din motarsu suka hango motar major tana tafiya a hankali ga dukkan alamu sun ƙaraso inda dr jazz Yake shiyasa suka rage speed din motar, bayan major yai parking din motarsu, kusan atare suka fito shida wani matashin saurayi dukansu suna asanye cikin kakinsu na sojoji, daga bayan motarsu Tiger yai parking din tasu motar, fitowa sukayi atare shida Sir mubarak, koda su Major sukayi arba dashi a hanzarce suka buga ƙafa tare da sara mashi, Jinjina masu kai Yai yayin da yake bin gine ginen da kallo Ya ce"ina ku ka ga jazz din Ya shiga"? Ya jefa masu tambayar cikin ƙagara da sonjin amsarsu.


  Major yace"Wancan gidan mai jan gate Ciki Ya shiga" yai maganar yana nuna wani katafaren gida, Da sauri Sir mubarak Ya nufi gate din, Major da Army din da suke atare kowannansu Ya zaro bindigarshi, shima Tiger Ya curo tashi pistol din, gefe da gefen sir mubarak Suka Jera sun saita bindugunsu saboda tsaro gudun kada akawo masu hari tunda basusan adadin miyagun da yake mu'amala da su ba, Cikin sanɗa suke tafiya suna bin ko'ina da kallo, ta ƙofar jikin gate din da aka bari abuɗe suka shiga, babu kowa abakin gate din tamkar anyi shara, Sir mubarak yace"Anya major akwai mutane acikin ginin nan? Naji shiru babu motsin komai, kodai kunyi kuskurene"? Girgiza kai major yai"Yalla6ai tabbas cikin ginin nan ya shigo, ba mu yi kuskure ba, akan idonmu  ya fito daga cikin motarshi Ya buɗe gate kafin Ya koma ciki Yajata zuwa cikin gida" 

Gyaɗa kai sir mubarak Yai"okey mu ƙarasa ciki" kaitsaye suka nufi katafaren ginin da suke tsammanin zasu samu hanyar shiga cikin gidan, adai dai bakin wata ƙofa, suka dakata A hankali Major Ya turo ƙofar cikin sa'a suka sameta abuɗe, ɗaya bayan ɗaya suke shiga, Hadadden palour ne An ƙawata shi da furniture, ga sanyin A.c ta ko'ina mai ratsa fatar jikin mutun.

  Sunyi mamakin ganin babu kowa a palourn, ko motsin mutun babu, daga cikin falon akwai bene da zai kai mutun up stair, yanke shawarar haurawa saman benan sukayi, Cikin sanɗa suke tafiya kowa ya saita bindigarshi saboda tsaro, a second floor suka dakata da yin tafiyar suna bin ko'ina da kallo, ƙofofin ɗakunane ta ko'ina, Sam sun kasa motsawa saboda sunfara kokwanton anya akwai mutane agidan

  Tiger yace"shirun yayi yawa, kada fa ace tarkone aka ɗana mana don mu afka"

  Major yace"ai shi soja da kasada akasanshi, Idanma tarkon ne suka shirya mana to bamu bane zamu rufza aciki ba, sune zasu afka, wata'kil watan tonuwar asirin su ne Ya kama"


  Sir mubarak Ya natsu Yana sauraronsu, ya rasa madafa sam bayason suyi kuskuren shiga gidan mutane, don ya fara kokwanto.

  Army yace"yakamata mu fara dudduba ɗakunan nan wata'ƙil mu same shi aciki" Ya furta hakan tare dakai hannu Ya buɗe ƙofar ɗaki Ɗaya,  karaf idanuwanshi suka sauka akan matasan Ƴan matan dake akwance saman bedmattress, cikin shiga ta kayan bacci"a matuƙar ruɗe ya juya yana kallon Sir mubarak Ya furta"yalla6ai ƴan matane kwance saman gado, Anya kuwa bamuyi kuskure ba"! Matsawa sukayi zuwa bakin ƙofar da Army yake a tsaye, kowan nan su Ya leƙa Sun yi mamakin ganin kyawawan ƴan mata kwance suna sharar baccinsu farare tass dasu kamar jinsin larabawa.

  Rai amatuƙar 6ace sir mubarak ya dubi Major"kace min nan jazz ya shigo to yana ina? Waɗannan ƴan matan alamace dake nuna cewa Gidan wani ne muka faɗo"

 Tuni major yasha jinin jikinshi, Muryarshi adabarbarce ya furta"yalla6ai wallahi da idona naganshi Ya shigo gidan nan, Ga army nan ka tambaye shi, ai tare dashi muka shigo, kuma shima yaga jazz din" Yai maganar yana nuna army da hannun shi

 Kallon Army sir Mubarak Yai, da kakkausar murya ya furta"idan har kukasa naji kunya wallahi zakuji ajikin ku ne" hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, Jin abunda yace masu, Guntun tsoki Yaja tare da juyawa da niyar Ya fuce daga gidan, kwatsam ba zato ba tsammani, kunnuwansu suka soma Jiyo masu shessheƙar Kukan mace cikin murya mai ƙaraji take fasa ƙara tana fadin"Bana so! Ka ƙyaleni Nace maka banaso, Ni ka ƙyaleni, ka sake ni ka rabu dani...." sautin gigitacciyar ƙarar data fasa gaba ɗaya Ya cika ginin, Kallon juna sojojin sukayi kafin da gudun gaske suka nufi Hanyar da suke jiyo sautin kukan Yarinyar, Sir mubarak kamar zai yi tuntube, cikin zafin nama suka haɗa ƙarfi wurin bangaje ƙofar ɗakin, A tsiyace ƙofar ta bude, Hankalin sir mubarak Idan yai dubu to ya tashi, A matuƙar gigice sojojin suke kallon abun da ke faruwa, Lamarin yai matuƙar ɗaga hankulansu, musamman Sir mubarak Ya gaza yadda da abunda idanuwanshi suke nuna mashi, Tuni zufa ta soma wanke fuskarshi, 

 Sam baiji motsin shigowar mutane ɗakin Ba, Ya duƙufa akan abunda Yake aikatawa, Rigar shaddar shi da wandonshi gaba daya suna asaman floor, Singlet ce kaɗai a jikinshi sai gajeran wando Fari, Ya haɗa uban gumi, matashiyar yarinyar daya danne saman gado sai kuka take Yi, tana bugun bayanshi da hannayenta, A wahalce take harba ƙafafuwanta cikin fitar hayyaci kamar ranta zai fita, ta gama galabaita, tuntana kukan neman agaji har muryarta tafara disashewa, wani irin kukan kura sir mubarak Yai cikin zazzafan taku Ya kutsa kai Cikin ɗaki, da hannayenshi biyu ya damƙo wuyar singlet din Jazz da ƙarfin gaske Ya wurgar dashi kasa gaba ɗaya ya kife kanshi ya daki tiles, Jiki na kerma ya ɗago yana dubansu ɗaya bayan ɗaya kafin ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Sir mubarak dake tsaye kanshi tamkar mayunwacin zaki, hankalinshi yai matuƙar tashi da ganinsu duk yabi ya ruɗe ya susuce, jikinshi ya hauyin kerma, sai faman zazzare idanuwanshi yake Yi, Muryarshi na kakarwa ya furta"daddy...." bai ƙarasa maganar da zaiyi ba, Sir mubarak Ya damƙo wuyanshi ya ɗago dashi tsaye cikin rauni na murya ta wanda ya karaya yake fadin"Jazz ka kasheni, Ka cuceni, dama abunda kake aikawata kenan? Ƴan mata kuke tarawa acikin gida, donku lalata rayuwarsu sannan ku kashe su? Nasha kama ka kanayin waya kana fadin kaji ashe mutanene kajin, Inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un" cikin jin ƙunar rai yace"Wallahi baka isa ka ɗaura min hawan jini baa, Kafin ka kasheni ni zan fara kasheka don ubanka, Mugu azzalumi fasiƙi, Jazz ka bani mamaki, ka cuce ni kuma ka cuci mahaifiyarka,' Cikin shessheƙar kuka Sir mubarak Yake furta maganar, Ya shaƙe wuyan Jazz sai faman mutsu mutsu yake Yi, don ya ƙwaci kansa.


Yayin da sojojin suke a kewaye da gadon da yarinyar take, duk tabi ta tsorata jikinta sai kerma yake Yi, short gown ce a jikinta, yalwatacciyar baƙar sumar kanta duk ta rufe gefe da gefen fuskarta, tamkar wadda tasha gudu sai faman yin haki take Yi.

   Sautin ƙarar da jazz Ya fasane Ya janyo hankulansu ga duban shi, wani irin radadin azabane Ya ziyarce shi sakamakon buga kanshi da sir mubarak Yai jikin Mirror din dakin, gaba ɗaya madubin Ya zube, Jini Ya wanke fuskar Jazz hatta gaban farar shirt din jikinshi Yayi ca6a ca6a da jinin shi, daddafe kanshi yai da hannu bibbiyu cikin mawuyacin hali Yake sambatu "Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Daddy ka kashe ni, Na shiga uku na bani na lalace, daddy ka rabani da rayuwata" 

  Yarinyar dake zaune saman gadon, ganin yadda suka raunata shi yasa ta fasa ƙara da ƙarfi ta furta"yaya Jazz, Wayyo Allah na kun kashe min shi, mugaye azzumai baiyi maku laifin komai ba amma kuna cutar min dashi" Da gudun gaske ta duro daga saman gadon ta kife ƙasa, sam babu natsuwa atare da ita, da rarrafe ta ƙarasa gabanshi, Ta sanya hannu biyu ta ɗago dakanshi ta daura saman laps dinta, Cikin shessheƙar kuka take fadin"Wallahi Allah bazai barku ba, Ku baku da burin daya wuce ku cutar da rayuwar waɗanda basu ji ba basu gani ba, Sai Allah ya saka mashi, ku dukanku sai kun shiga wuta" ta fada tana nuna su da yatsan hannunta, kallon juna sojojin sukayi, sunyi matuƙar girgiza da jin kalaman Yarinyar, sun fara kokwanton Anya kuwa Zargin da sukeyi mashi gaskiya ne? Tayaya yarinyar da ake cutar da rayuwarta, kuma take fada don an ta6a mutumin dake ƙoƙarin rabata da mutuncinta!! Fashewa tayi da kuka Hannayenta tuni sun 6aci da jinin dr jazz tana kuka tana ambaton sunanshi"yaya jaz dan Allah kada ka mutu kabarmu, wallahi idan ka mutu nima saina kashe kaina"

  Zuciyar sir mubarak ce ta soma harbawa da ƙarfin gaske, Jiri ya soma ƙoƙarin kwasarshi, Gaba ɗaya ya gama rikicewa, Hankalinshi atashe Yake kallon Kwalaben alluran dake ajiye saman bedside drawer tare da sirinji, hada magunguna, Adaddafe Ya nufi drawer din da niyar Ya duba kwalaban don ganin na menene, sautin ringin wayar Jazz ne Ya dakatar da shi, da sauri ya daura rinannun idanuwanshi inda yake jiyo sautin daga cikin aljihun wandon shaddarshine, Major ne yai saurin daukar wandon Ya binciko wayar cikin aljihun, Ya miƙa ma sir mubarak, yatsun hannun shi na kerma ya ruƙe wayar, batare daya duba sunan mai kira ba Yai picking call din Ya sanya kiran handsfree.

 

  Sautin muryar mutumin dayaji tayi matuƙar gigitar dashi, har baisan sa'adda Ya saki wayar jazz ta fadi saman floor, sojojin dake atare dashi duk sun sha jinin jikinsu, kallon kallo suka soma Yi a tsakaninsu, cikin matsanancin tashin hankali, sautin shessheƙar kukan matashiyar ya cika dakin, dr jazz tuni Ya jima da sumewa.


*EX-PRISONERS💔* 

     

Gaba ɗayansu sun hallara a dining room, domin cin abincin Dinner dinsu, mutun ɗaya ne ke babu acikinsu, Yana can dakin shi, mazan suna fuskantar matan, sunyi shiga kala ɗaya wandon jeans da farar shirt,matan kuma dogayen rigunane a jikinsu, Aunty ummi ce kaɗai ta banbanta dasu, riga da skirt ne ajikinta sun matseta, shape din jikinta Ya bayyana muraran, babu mayafi akanta, sa6anin su Batul da sukayi rolling veils.


tunda suka zauna Unaisah ta kasa samun sukuni, yanayinta tamkar na mara lafiya, sai faman jujjuya spoon take Yi acikin plate din gabanta, da ke shaƙe da abinci, damuwar duniya ta isheta, sam babu sukuni akan fuskarta, A hankali ta ɗago da ido tana duban fuskokin Ƴan uwanta, tun daga kan Sajeed dake fuskantar Azeeza, suna cin abinci suna kallon juna, har zuwa kan Haris dake fuskantar Hannah, kafin ta kawar da idonta daga kansu ta maida su kan fuskar Naufal da javed, sun natsu suna cin abincinsu, hasken musulunci ya fara shigarsu, komai nasu cikin natsuwa suke yin shi,  mayar da idanuwanta tayi akan face din jamimah, bakinta duk ya 6aci da maiƙo, ta samu cinyar kaza saici take Yi kamar tsohuwar mayya, ta cinye tsokar naman, Ƙashin take gwaigwaya kamar babu sauran naman alhalin gashinan saman tray guda aka jera masu chicken legs, girgiza kai tayi kafin ta mayar da dubanta kan Batul dake gefenta, ita dai duniya babu abunda ke burgeta irin taliyar indomie, tun ranar farko data fara cinta, kullum ne in zasu ci abinci saita ci ta, sam bata gajiya, da hannu take nannaɗota kafin ta tura abaki, rantane ya raya mata ana kallonta, dai dai time dinda ta tura taliyar abaki ta ɗago da ido suka kalli juna ita da Angel, da sauri ta haɗiya taliyar, cikin muryar raɗa ta tambayeta lafiya take kallonta? Ko tayi ƙauyancine"? Girgiza kai Angel tayi babu komai kawai burgeni kikeyi idan kina cin noodles da hannu"

 Gyaran murya ummi tayi masu atare suka ɗago suna kallonta.

 "Unaisa tun ɗazu na lura kamar bakya jin daɗi, meke damunki ne"? Murmushin yaƙe ta sakar mata"babu komai aunty ummi, ko kinga wani abu ne" ɗaga mata gira tai"ƙwarai kuwa, tun da gashinan kin kasa cin abincinki"

Kafin unaisa ta ƙara furta wani abu, Muryar Haris ta katse su

  "Kodai Danish bashi da lafiyane? Tun jiya da rana ban ƙara ganin ya leƙo waje ba, naso naje na duba shi sai dai karatu Ya mantar da nayi yin hakan" 

  Cikin nuna damuwa Sajeed yace"wallahi yana araina, tun ɗazu da muna awurin kar6ar karatu nake ta tunaninshi, bansan dalilin dayasa baya son zuwa cikin mu cin abinci ba, naga dazu da rana ke kika kai mashi lunch dinshi a dakin shi" ya faɗa yana nuna Unaisah da spoon din hannunshi.

  Naufal Yace"to me zai hana mu tashi muje ɗakin nashi mu duba su? Ni abunda ke damuna da danish baya son sakewa cikin mutane" Yai maganar fuskarshi dauke da damuwa.

 Javed yace"ai halinshine tun fil azal, kaima kasan Danish bai cika son zama cikin mutane ba, baison surutu kuma baison ana kallon shi"

  Gyaran murya Ummi tai masu, Hankalinsu Ya dawo kanta sun natsu suna jiran jin me zatace

  "Koda ace halinshi ne hakan bai kamata ku ƙyale shi ba, cos barinshi acikin ɗaki zai Iya haifar mashi da wata damuwar, duk da naga Unaisah tana ƙoƙarin dubashi, amma a ƙalla yakamata kuma kuna zuwa wurinshi kodan ku dinga ɗebe mashi kewa, kafin zuwa lokacin da zai saki jikinshi, nasan rashin sabone ke damun shi"

  Jinjina kai sukayi alamar gamsuwa da bayaninta, Sajeed yace"ku tashi muje dakinshi Inyaso sai mu tafi da kayan abincin mu ƙarasa ci acan" Yai maganar tare da miƙewa, da sauri Unaisa tace"a'a basai mun tafi mu duka ba, Ku zauna ni zanje in taho da shi" amsa mata sukayi da toh, da sauri ta miƙe ta nufi ƙofar fita daga dining room din

 Miƙewa Batul tayi Ummi tace Ina zuwa? Cikin sanyin murya tace ina so zanbi Unaisah ne"

 "Ki koma ki zauna, ai tace zasu dawo atare dashi ko"? Amsa mata tai da toh jiki asanyaye ta koma ta zauna.

   Shiru suka ɗanyi, abincinma sun dakata da cin shi, hakanan suke jin zuciyoyinsu na bugawa, Jemimah kadaice ke cin abinci ta cika masu kunnuwa da sautin taunar abincinta, da gangan take yi duk don ayi mata magana.

   Harara Azeeza ta watsa mata"dan Allah ya isa haka, ba zaki Iya ci a hankali bane"? Hanna tace"ki daina wahalar da bakinki, dagangan take yi duk don ayi mata magana" tuntsirewa tayi da dariya tana fadin"Eh din kuma gashi kunyi min maganar ba" girgiza kai ummi tayi fuskarta dauke da murmushi take dubanta, hankalinta kwance take yin magana. Kallon da naufal ya jefa matane yasa tai shiru tana ƴan ƙunƙuni.

  "Kuna burgeni, gaba ɗayanku" ta fada tana nuna su da spoon din hannunta.

 Batul tace"aunty ummi, kina nufin kina sonmu"? Jinjina mata kai tayi"haka  nake nufi," murmushi su naufal suka saki jin abunda tace, 

  Parveen na faman siɗar hannu tace"Aunty ummi ke baki haifi ƴa'ƴa bane, kamar yadda daddyn unaisah ya haife ta? Ko kuwa ita mace bata haihuwane sai maza"? Da mamaki Ummi ta dan zaro ido tana kallon parveen da tayi maganar, sam babu wasa akan fuskarta ita bilhakki take Yin maganarta.

  "Amma baki da hankali parveen, Kin manta labarin da unaisa ta ta6a faɗa mana ne? Macace take haihuwa ba namiji ba, itama Mommyntane ta haifeta ta jefar da ita cikin wannan abun kalar na toilet din gidan nan, namanta sunanshi" Batul ce tai maganar,

 Azeeza tace"eh kuwa hakane, Macace ta haifi unaisa ba namiji ba, to aunty ummi ke kin ta6a haihuwa"? tayi tambayar tana kallon ummin america wadda mamaki da al'ajabi suka cikata, sai kallonsu take Yi ɗaya bayan ɗaya, sajeed Ya duƙar da kanshi ƙasa sai faman sakin murmushi yake Yi jin wautar parveen.

  "Aunty ummi kinyi shiru baki ce komai ba, kina ta kallonmu" Hanna ce ta jefa mata tambayar, ta ƙura masu ido tana binsu da kallon mamaki, 

 "wai kuna nufin bakusan komai ba, game da zamantakewar aure?

Atare suka haɗa baki wurin furta"Aure kuma"? Gudun kada suyi wata 6aran 6aramar yasa Sajeed yin saurin cewa"aunty Ummi, Yakamata mu maida hankali akan abunda muke Yi yanzu," Ta6e baki taɗanyi kafin ta furta"okey, " ta fahimci baison maganar dama ta lura yafi su hankali shida Unaisah, bata ta6a ƙagara da sonjin labarinsu ba sai yau, tabbas tana son tasan tarihin rayuwarsu! Ya akai har suka kai wannan shekarun basusan komai dangane da zamantakewar aure ba? batun Yauba ta lura da ƙarancin wayewarsu, kamar babu ƙwalwa akansu, basu iya komai ba, In banda cin abinci da kwanciya bacci sunfi ƙwarewa a 6angaren nan.


 _(Ummin america batasan su wanene prisoners ba, Mutanan da suka juri rayuwar kulle tun suna jarirai, basu ta6a ganin hasken rana ba, dare da rana basu da abunyi daya wuce idan ankawo masu abinci sau ɗaya suci sai kuma idan lokacin baccin su Yayi su kwanta, badan Allah Ya ƙaddara zuwan unaisah kurkukun ƙaddara ba, da kuwa  abunda zasu aikata sai yafi hakan saboda su din tamkar baƙine a duniyar mutane, basusan komai ba, unaisah itace ta wayar masu da kansu dangane da mutanan duniya da wasu abubuwan da suka shafi rayuwar ɗan adam shiyasa ma har suke Iya sakin jiki suyi rayuwa acikinsu)_


Shin meya faru bayan Unaisah ta fita daga Dining room?


  Cikin sauri ta nufi upstair, tunkafin ta ƙarasa ƙofar ɗakin danish ta dinga jin faɗuwar gaba, tamkar zuciyarta zata faso ƙirjinta, jiki na rawa ta nufi ƙofar room dinshi, zura ƙafarta keda wuya cikin ɗakin, taga babu kowa wayam har saman gadonshi babu mutun, sai faman baza ido take Yi tana faman ambaton sunanshi tamkar makoshinta zai 6allo"Danish! danish! my Man! Kana  ina"? Shiru babu alamun zai amsa mata, ƙofar toilet dinshi ta tunkara lokaci ɗaya taji sautin gurnaninshi mai matuƙar firgitarwa ya cika ɗakin, cikin jin faɗuwar gaba ta sanya hannayenta biyu da ƙarfi ta ingiza ƙofar ta buɗe, tun daga bakin ƙofar toilet din ta ci karo da singlet dinshi, A hankali take bin ko'ina da kallo har tayi nasarar cin karo dashi kwance acikin kwamin wanka, wanda ke akewaye da glass, ya ƙunshe kanshi cikin kwamin, jikinshi sai kerma yake yi, faɗawa cikin toilet din tayi, Cikin sanyin murya take fadin"My man meke damunka? Meyasa kake yin gurnani? Baka da lafiyane" idanuwanshi dake a lumshe ya buɗesu sun kaɗa jawur dasu tamkar an wanke ƙwayar a cikin jini, Hankalinta ba ƙaramin tashi yai ba, sam bata damu da yanayin da zata riske shi ba, Jiki amace ta shiga inda kwamin yake ta zuƙunna agabanshi tana dubanshi, fatarshi tayi wani irin haske naban mamaki, Ya cika kwamin da ruwa mai sanyi, amma saboda tsabar zafin jikinshi yasa ruwan ya koma na zafi.


  Idanuwanta tuni sun cicciko da ƙwalla muryarta na rawa ta furta"My man dan Allah kayi min magana meke damunka? Meyasa ka shigo toilet ka kwanta cikin bathtub"? Ta faɗi hakan ne donta fahimci ba wani uziri bane ya shigo dashi toilet dinba, saboda bai cire short dinshi ba, Ahaka ya shiga cikin ruwan duk don ya sassauta zafin da jikinshi yai mashi.

   Da wata irin kakkausar murya ya furta"Kiyi nesa dani, zan iya cutar dake, bani bane, Ki tafi ki ƙyaleni, bana so in ta6a lafiyar jikinki" zazzare idanuwanta tayi waje tamkar ƙwayar idanuwan zasu faɗo ƙasa, muryarta adabarbarce ta furta"me..meyasa kace haka danish? Idan bakai bane to wanene? Nashiga ukuna! dan Allah kadaina furta waɗannan kalaman, Ni nasan bazaka Iya cutar....." kasa ƙarasa maganar tayi sakamakon ganin sa6ar macijin dake tsastsafo mashi saman fatar wuyan shi, Kafin ƙyaftawar ido danish ya rikiɗa ya zama Giant snake fari sol, Jikinsa yana da tsayi da kauri, mai santsi, Ya nannaɗe kanshi cikin kwamin wankan, Wani irin narkeken maciji danƙareran gaske yana da doguwar jela da siraran harshe, tsabar firgici da ruɗanin ganin abunda bata ta6a ganiba Ya hanata motsawa, jikinta ya hauyin kerma zufa ta wanke fuskarta, ko amafarki bata ta6a ganin mutun ya rikiɗa ba sai yau da Allah Ya nuna mata Danish ɗinta Ya canza halittarshi zuwa maciji, girgiza jikinshi yai nan take kwamin wankan da yake acikin shi Ya tsastsage Ya tarwatse, Ya faɗo ƙasa, aikuwa da gudun gaske Unaisah ta fito daga dakin, ta fasa razananniyar ƙara, tana gudu haɗi da yin tuntu6e, a matuƙar gigice ta fado saman bene, Mayafin kanta tuni yajima da barin jikinta, Sumar kanta duk ta rufe fuskarta, cikin tashin hankali take tattaka matakalar benan, tana kuka haɗi da ambaton sunan ƴan uwanta

  Adai dai lokacin Chief Owais Yana saukowa down ta cikin glass elevator, ya kimtsa cikin Dark jeans, daga sama ya sanya button-down shirt, yayin da ƙafafuwanshi ke asanye cikin patent leather shoe, gefenshi Big guy ne hannunshi ruƙe da car key, karaf idanuwan big guy suka sauka akan unaisah dake Faman zumbula gudu tana tunkaro down, ta cikin glass elevator din yake kallonta, kafin yai yunƙurin buɗe baki Yai magana, unexpected danƙareran macijin Ya kunno kai daga ɗakin ya daka tsalle Ya haura ta saman handrail din benan Ya rigata saukowa ƙasa, da buɗar bakinshi sai cewa yai"yalla6ai anya ban fara samun matsalar gani ba kuwa? Kodai tsufane Ya fara kamani"?

*✍️ Mu haɗu Jibi In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya, Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*

First bank

3196407426, 

 Bature Hafsat Muhammad

Post a Comment

You can ask a question about something you don't understand about our website via comment or you can send us a story through this email thevoice24ng@gmail.com. You can contact us Directly using Contact Us page.

Previous Post Next Post